[4/4, 6:49 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
SADY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
HAFSAT ISMA’IL (MMN HANEEP).
Bismillahirrahmanirrahim
Godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata Ala daya bamu ikon fara rubutu lafiya ina rok’on Allah yasa mu gama lafiya, Ameen.
1_Babbar rigar sa ya sab’e tare da sa hannu ya bankad’e labule idonshi akan uwargidansa wacce suke kira da Mamy. Da d’an jimami ya soma magana
“Kinga mutanen nan ko? har yanzu shuru ba busu babu dalilin su.
Baki Mamy ta d’an ta6e
“Uhm to ni meye nawa a ciki Alhaji? In dai Khadija ce toh idone nawa in an maimaita irin ta wancan karan..
Da sauri ya daga mata hannu tare da fad’in
“Kar ki mana mugun fata,tuntuni nake fad’a miki wannan zantutukan naki su suke tasiri akan Deeja”..
Baki taja ta rufe fuskantar bazai gane inda ta dosa ba.
“Ka d’ai kirata ka ji ta bak’inta, dan na tabbatar tasan abinda ta kulla..
Jim yai tare da sawa Mamyn ido,zancenta da kamshin gaskiya,dan haka wannan karan sai ya kwala kiran Deejan.
Da nutsuwa ta fito fuskarta babu yabo babu fallasa ta zauna gaban iyayen nata.
Abba ne ya gyara zama tare da fad’in
“Nace ya kukai da shi Aminun kinji da kyau kuwa yau din za suzo akan maganar auren naku?”.
Kai ta dago tare da d’an sato kallon Mamy dake kallonta sai tai da kai kasa.
“Abba ni banyi waya dashi ba tun shekaranjiya, jiya ma naita kiransa kuma bai d’aga ba…
“Hmmm,kuma dai..
Mamyn Abba ya kallo
“Meye na wani hmm? Kinga indai bazaki fadi Alkairi ba to kiyi mana shiru”.
Hannu ta aza bisa bak’inta halamun tai shiru.
Shi kanshi Abban al’amarin Deeja na bashi ciwan kai,sai dai so ya hana ganin laifinta.
“Ni fa bansan me naiwa Aminu ba shekaranjiya k’alau muka rabu dashi da yamma wallahi Mamy”..
Baki Mamyn ta ta6e halamun meye nata aciki duk Abban na kallon su.
Chan dai ya ce
“Kinga bani lambarsa nakirashi da kaina, in aka bibiya ma suna hanya gosulo ya tare su”…
Baki Mamyn ta saka tana duben Abban lokacin da Deejan ke miko mishi waya d’auke da numbern Aminu bisa screen.
Aminun ya kira,sai dai har ta gama ringin ta katse Aminu bai dauka ba har karo na uku.
Cike da mamaki ya sauke wayar tare da ciro tashi ya hau diban numbern zuwa tashi.
Deejan ya mika wa tata tare da sanya tashi bisa kunne halamun calling.
Bugu d’aya biyu Aminu ya d’aga wayar wanda ke kwance saman gado ya tasa hotunan Deeja a gaba yana jero mata Allah ya isa tun a daren jiya.
Sallama yai yi cikin sassanyar murya,take Abban ya shanye mamakinshi ya amsa sallamar.
Daga can b’angaren Aminu ya gyara zaman wayar a kunnan sa
“Wa ke magana?”.
Cike da kunar rai Abba ya ce
“Isma’il ne Mahaifin Khadeeja…
Mike wa Aminu ya yi cike da girmama wa yana gaida shi.
Sassauto wa Abban yai tare da amsawa,
“Dama munji shiru ne ga jama’a na jira daga chan gurin naku..
Jim Aminun ya yi,bai isa ya cewa Abba kanshi tsaye ya fasa auren Deeja ba,dan haka sai ya hau kame-kame
“Um dama Abba cewa nai a bari na kuma shisshiryawa a tsanake in yaso in Allah ya kaimu wani watan sai naturo ayi maganar auren ina neman wannan alfarmar Alhaji”.
Jim Abban yai,tuni ranshi har ya fara kuna jin zancen Aminun naso ya mayarshi karamin yaro,dan haka ya ce
“Shekara biyar tayi maka?
Kai Aminu ya girgiza da sauri kamar Abban na kallonshi
“A’a Abba,hak’uri za ayi akwai shirin da nake yi insha Allahu…
Kit ya kashe wayar ba tare da ya jira zancen Aminun ba rai na tafasa,tabbas yasan karan nan ba laifin Deeja ba ne.
Kallota yai yadda ta fara waro ido tana kallonshi.
“Ke dama wannan yaron d’an k’ananun mutane ne masu baki biyu baki sanar da niba tun wuri sai da na tara jama’a yanzu?
Kasa tai da kai, sai ya kallo Mamy wacce nata ido da kunnuwa.
“Mey zanje na cewa mutanen nan?
“Tabbas wannan abu akwai rashin kyauta wa aciki.
“Alhaji.
Ido ya sa mata
“Ya fa kamata ka tuhumi Khadija ko akwai tsiyar da ta shukawa yaron nan,ni nasan Aminu yaron kirki ne kasan babu yanda za ayi haka kurum yace ya fasa auren nan..
Ido Deeja ta zaro tare da kallo Abban,haka yasa a hassala ya ce
“Mey ki ke nufi kenan? Kina nufin laifin Khadija ne duk da kinji abinda ya ce?
Kai Mamyn ta girgiza tare da fad’in
“A’a, ni bance ba,dan haka Allah ya baku hak’uri..
Fuska Deeja ta marairaice tare da yin narai-narai ido kamar za tayi kuka
“Abba,wallahi ka yarda bansan me naiwa Aminu ba shekaran jiya k’alau muka rabu fa…
Harara Mamy ta doka mata cike da takaici,kan ta kai ga magana Salis ya shigo.
“Abba su Baba Zubairu fa sun k’osa da jira.
Ajiyar zuciya Abban ya sau,nan ya sanarshi abinda ya faru.
“Abba to ajira shin kamar yanda ya ce d’in ko akwai matsalar data tsai dasu”.
Kai ya hau girgiza wa,
“A watan nan da nai alkawari a shi zan aurar da Khadeeja bazama takai watannin daya d’iba ba balle yayi tunanin jiransa ta zauna yi, in alfarmar yake nema meya hanashi ya nema tun kwanaki sai yau da muka zau…
Hannu Deeja ta aza bisa kai tana kallon Abba ido a ware wanda ke sababin zai bawa Aminu mamaki.
Tuni taji gabanta na fad’uwa ganin a yau tai gudin gara gashi zata tadda zago.
Mamy ta kallo wacce ke murmushi tana kad’a kai tare da bin su Abban da ido.
Tabbas yau karya ta k’are.
Sumumu ta mike tana tafe tana had’a hanya,
“Yaushe za a gane wai ni Deeja *INA DA BURI* ne?
Da6ar ta zauna bakin katifar d’akinta hawaye na zuba.
Hannu ta aza bisa kai tare da sakar ihun kuka na tuno da shin wa Abba zai bata?
Tasan ta kad’e har ganyenta in har aka bata wanda bashi take da buri ba.
****
Hak’uri Abba ya bawa yayun nashi da sauran y’an uwa had’i da sanar su abinda ya yanke,a take su ka goyi bayan shawarar kan a aurar da Khadija dan huce takaicin Aminu da ‘yan baya.
***
Futowar shi kenan daga d’aki kasancewar asabar ce ba zuwa aiki ya jiyo fad’an Mamyn, ko ba’a fad’a ba yasan itada Khadeeja ne don haka kai tsaye ya nufi cikin parlourn.
Kuka wiwi ya samu tanai a gaban Mamy,da ido ya bita yana mai kallon Mamy da halamun tambaya.
“Ai dama nasan bani da kaffara Kamal,tabbas Khadija na da hannu gurin rushe duk wani shiri na aurenta in har ya taso.
“Dan bani da abinda zan iya miki,dan fa duk tsuntsun da yaja ruwa shi ruwan kan doka..
Kai Deejan ta dago ido jajir tare da maka mishi harara,in har taki jinin wani a gidan,toh Kamal ne,dan haka cike da kara tusa haushi ya sau mata murmushin mugunta Mamy na kallonsu.
Tashi Mamyn tayi tare da yin hanyar kitchen, cike da keta ya kallota wacce har yanzu hawaye take goge wa kanta kasa.
“Irin ku ai dama a auren sadaqa ku ke karewa garin ruwan idon *INA DA BURI*..
Chak kukanta ya tsaya tare da kalloshi ba koh kiftawa.
Kai ya d’auke daga kallonta, dan haka sai tai murmushi irin wanda yau tare da fad’in
“Ban yi kama da matan da za ai sadaqa dasu ba kasan wannan.
“Sannan duk halina bai kai na mai auren auri saki ba dan haka bazai zama laifi ba in har na ce nima *INA DA BURI*…
Da sauri ya kallota,tabbas yasan magana ta ya6a mishi had’i da gori kamar yadda ta saba in taso sa shi a bakin ciki.
Yau ma kamar kullum yai tsam tare da kallonta,bai san meye laifin Babanshi zai rika zama makamin da za’a rika dukanshi dashi a kullum ba yana jin haushi..
Duk tsiya yasan iyaye-iyaye ne,ba kuma a sauya musu suna,dan haka yana jin ciwo in har Deeja ta ci mishi fuska akansu..
Murmushi ya yi tare da gyad’a mata kai.
“Hakane,zan so ya kasance a ni za a bawa sadakar aurenki Deeja.
Rai ta had’e kamar yadda yai tsammani da sauri,dan haka sai ya girgiza kai tare da fad’in
“Mai da wukar,dan koh a k’afa aka d’aura min ke bazan iya ja ba,sannan nima *INA DA BURI* bana jin kina daga cikin shi..
Tashi yai ya batta baki sake dan tsabar takaici, da kallo Mamy ta bishi wacce ta fito a kitchen sarai ta ji su har ya fuce.
Deeja ta kallo wacce ke kumfar bak’in
“Ubangiji ya tsareni ni Deeja,koh a mafarki ba za kaga wannan ranar ba wallahi, mugu kawai mai mugun fata..
Tashi tai tare da shiga d’akinta cike da kukan takaici.
Tsam Mamy tai tana tunanin wani abu cike da sarkakiya,kai ta jijjiga tana murmushi dan jin shawarar zuciyarta.
Ku jira mu.
By
{SAHAF}..✍🏾
[4/4, 6:49 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION
©(SAFHA)
FEENAT JAFAR
SDY JEGAL
&
HAFSAT (MMN HANEEP)
2_Idonta yayi jajir don tsabar kukan data sha, shikuwa Najib tsohon saurayin ta dake gefe yana faman aikin lalashin sahibar tasa, ya sauke gwauron numfashi kana ya ce
“Ni yakamata nayi kuka bake ba Deeja, ni banga ta inda Allah ya kuskuroni ba da kika kasa tsayar dani matsayin mijin aurenki.
Ido ta dago tana dubenshi galala,dan haka sai ya cigaba da fad’in
“Wai shin,ni soyayyar ce ban iya ba kome?
Wani mugun kallo ta sauke masa cike yatsine fuska.
“Ka ga,nifa ban kiraka don ka zauna kanaimin shirme ba, kabani shawarar yanda zanyi donni gaskiya bazan yarda ayimin auren dole ba dan wannan baya cikin buri na”.
Tsayuwa ya gyara,
“To ni yanzu mezan ce miki khadeja? Kawai kije kicewa Abba ni ki ke so kinga kin huta da fargabar Wanda za a aura miki…
Shiru sukai ganin Abba zai shige kowa ya saukar da kai kasa.
“Abba ina yuni..
Dan rissina wa yai Abban yana binsu da ido.
“Lafiya Najib,ya mutan gidan?
Har su ka gama gaisawa Abba na hasaaso wani abu cikin ranshi.
Kai ta dafe tare da fad’in
“Ya ilahi..
Fatan ta Allah yasa kar Abba yai wa zancen su na yau fassara,dan haka da sauri ta ce
“Kaga shikenan jeka inna nutsu zanneme ka,dan yau ba wani aikin da zaka min..
Kai ya kad’a yana mata wani kallo na Allah kai damo ga harawa ta shige ciki.
Kicibis su ka ci da Kamal a bakin kofar parlour duk su ka kallo juna rai a had’e.
Kauce wa ya yi da niyar ya bata guri itama ta koma inda ya koma,harara ta maka mishi da zummar sauya gu ya sake yin wajen dan haka a masife ta ce
“Malam ka ban waje na wuce..
Rai ya had’e ganin zata raina mishi hankali ya ra6a ta gefe ya wuce tana mishi harara.
****
“Ni fa ina ga yaran nan son juna suke Mamyn su..
Da mamaki Mamyn ta kallo Abba.
“Su wa fa?
Murmushi ya yi tare da gyara zama.
“Najib da Deeja nah..
Ido ta sa mishi,jin ba wanda ta hasaso ya hasaso ba.
“Najib kuma?
Kai ya jijjiga mata.
“Ina ga na samo mafita, abu d’aya nake tunani bai da aikin yi ban san da mey zai riken Deeja ba..
“Ni fa Alhaji ba Najib ya dace da Deeja ba,kamata ya yi ka had’a Deeja da wanda zai iya seta tunaninta ya juyata ba wai ita ta juya shi ba.
Ido ya sa mata yadda take bayanin,yasan inda ta dosa tunda an ta6o kishiyarta Deeja.
Dan haka da sauri ya katseta.
“Ban san mey Deeja ta tsare miki ba,kullum burinki ki ga yarinyar nan na kuka tamkar ba ke ki ka haifeta ba.
Baki ta saka tana kallonshi,daga fad’in gaskiyar?
Kai ta kad’a tare da jan bak’inta ta rufe,tasan yanzun tata zatai zafi.
****
Aure kam Abba bai fasa ba,duk wata dabararta ta kare daga Najib har Mariya kawarta ba mai wata shawarar da zata bulla mata.
Yau tafi kullum kuka ganin gobe iyanzu ta zama matar Najib.
Zumbur ta mike tare da fita a d’akinta ta nufi d’akin Abba,tabbas wannan ce damarta ta karshe,in ta bari aka aura mata Najib tasan tai babbar wauta a rayuwa.
Kuka reras ta tasa shi gaba tana yi,dan haka tuni ya rikice ya hau tambayar mey ne ne?
“Abba ni fa ka had’ani da kowa amma banda Najib…
Harshe ta datse jin ta kwafsa.
Murmushi Umman tai tana cigaba da dama furarta.
Kai Abban ya girgiza,
“Matuka zan sa6a miki wannan karan Deeja,dan babu abinda zai sa na warware auren nan tunda har gobe ne za’a d’aura..
Bori ta hau mishi harda su shusshura k’afa.
Ya sani da matuka yana ji da ‘yarshi tilo d’aya mace tamkar tsoka daya cikin miya.
In har ba so yake zancen Baba Zubairu ya tabbata ba na tsoron Deeja yake toh kwa dole ya nuna mata aure ba fashi,dan haka kawai sai ya tashi tare da shige wa band’aki ran shi na kunar jin kukan nata.
Rarrafo wa tai gaban Mamyn.
“Dan Allah Mamy ki taimake ni kar a ban Najib,ni wallahi nafi karfin Najib,na yarda ni nake korar samarina amma dan Allah kar a ban Najib..
Baki Mamy ta saka,fatan ta Allah yasa Alhaji yaji wannan batu na Deeja.
“Na sani ai,ki d’auka wannan ne sakayyar su gare ki da Allah zai musu,baki fara kuka bama sai in kin ganki a gidan Najib din.
Kuka kam Deeja tasha shi,hannu bisa kai ta fio a dakin Abban.
Duk da kallo su ka bita duk su na sauraron ihun nata daga saman Abban.
Murmushi Kamal ya yi tare da girgiza kai.
A gaban yayun nata ta zube.
“Ya Salis dan son ku da Allah kar ku bari a min auren nan da Najib,wai ni yau Abba ya fatattaka…
Kuka ta sa musu,dan haka masu harararta nayi,masu kunshe dariya nayi.
A kaf gidan da wanda bai san halin Deeja bane,ai a ganin su wannan ne dai-dai tunda dama bata da abokin shawara sai Najib,dan haka a hankali kowa ya fara zame wa tana binsu da ido.
Kamal ne kad’ai ya rage wanda yasha mur yana kallonta.
Harara ta sau mishi duk da kuka take kamin ta mike tana goge hawaye zata wuce
“Ni kad’ai zan iya taimakon ki Abba ya janye auren Najib kin san wannan..
Chak! Taja ta tsaya ba tare da ta juyo ba,ta sani da tabbas matuka Abba yana jin shawarar Kamal.
“Ki sauke komai ki bishi ya taimake ki..
Kai ta kad’a jin shawarar zuciyarta.
A hankali ta juyo tana mai goge hawaye.
Ya hakimce a kujerar tamkar wani sarki yana dubenta,wannan ce yasan damarshi ta karshe da lalle Deeja zata shigo hannunshi.
Kasa ta zauna tare da kura mishi ido.
“Toh ka taimake ni..
Kallon tara saura kwata yai mata.
“Wannan ba ladabin roko bane..
Harara ta sau mishi tana had’e rai,sai dai tuno da shine damarta ta karshe yasa ta mike bisa gwiwarta tare da yin kalar tausayi da yanayin roko
“Dan Allah ka taimake ni yaya Kamal..
Murmushin mugunta ya saki tare da jijjiga kai ya mike
“Ashe kin iya ladabi yarinya..
Wuce wa yai ba tare da ya sake kallonta ba saman Abba,cike da takaici ta mike ji take tamkar ta shako shi ta huta,sai dai dole tai ladabi dan ita zai taimaka.
By
{SAFHA}.
[4/4, 6:49 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).
3_Washegari sai baza ido take taji ance an fasa aure shiru,sai ma shiri da kowa taga yana yi baki a washe.
Gabanshi ta sha ganin yana neman fita tana dan satar kallonshi ganin sosai yau yai kyau tamkar ango.
“Ina kwana..
A ciki-ciki ta gaida shi,murmushi yai tare da hard’e hannu yana kallonta.
Baki ta zumburo jin yai mata banza da wannan munafukin murmushin nashi,dan haka sai ta hau yatsina tana fad’in
“Ni fa ban gane ba,koh ka fasa taimakon nawa naga kowa na shiri?
Tsayuwa ya gyara yana kallonta,dan haka tuni ta sake kulewa.
“Ladabi shi yai miki karanci..
Rai tai saurin had’e wa tare da mishi kallon sama da kasa cike da kar ka rainan hankali..
Ajiyar zuciya ya yi tare daga kafad’a
“Koh da yake,kar kiji komai,na gama taimakon ki tunda kin roka jiya,ki sa ido babu aurenki da Najib Insha-Allah..
Fuska ta saki ganin ya juya ta sake yin saurin shan gabanshi,Abba da ya sakko yana kallon yadda take farin ciki,hala koh ta san abinda ke gudana?
Murmushi ya yi ganin yadda Kamal din ma yake mata murmushi har ya fuce.
Juyo wa tai,da mamakin shi harda gaidashi ta shige d’aki,ita fa a dole sunyi wa Abba wayo.
Ta sani Kamal in ya ce toh ya ce,bai da karya a lamuranshi,dan haka tasan aure babu.
Da kallo kawai Mamy ke binta ganin yadda take rawar kan,sai ta girgiza kai da murmushin mugunta,tasan karyar y’arta kam ta kare.
Dan haka da ido kawai take binta.
Kasantuwar aure babu wani shiri yasa gidan ba jama’a sosai,har kawayenta ta ce kar wanda yazo.
Kasantuwar a unguwar Baba Zubairu ake taro bata san wainar da ake toya wa ba sai da suka dawo kusan sha biyun rana.
Tana d’akin Mamy sai alkawari take mata akan Insha-Allah ta kusa samun cikar burinta tai mata adu’a kawai.
Kai Mamyn ta kad’a tana murmushi, kai daga gani na baki da wayo ne.
Yayunta ne suka shigo da sallama,kowa bakin nan har k’unne.
“Kun dawo?
Kai su ka jijjiga
“Eh Mamy.
Deeja su ka kalla tare da fad’in
“Congratulations toh Deeja…
Baki ta wage harda fad’in
“Thanks..ina yaya Kamal?
Leko wa yai yasha shadda fara ganin d’akin ya cika bai shigo ba.
Hannu ta daga mishi tare da fad’in
“Na gode
A hankali.
Kai ya karkatar halamun u r welcome.
“Ai Najib Mamy yana chan sai bori yake wai akan ba dashi aka d’aura ba sai da wani…
Da sauri ta kallo Salis wanda ke magana.
“Ban gane ba?
Kallonta su kai ganin yadda ta sa mishi ido.
“Kwarai, ba’a d’aura da Najib ba,na cikin gida akai..
Ido ta zaro tare da fad’in
“Waye wani?
“A ina yake?
“Kamal man,waye na cikin gida in ba shi ba…
Kamal din ta kallo da sauri cike da tuhumar haka mukai da kai? Tana had’iye wani d’ad’d’acen yawu jiki na ka’rkarwa,a zabure zatai kanshi taji ta kasa motsi ganin yana mata murmushin mugunta,kan ta farga har ta fara ganin duhu.
A hankali ta fara tangad’i kowa hankalinshi yai kan Mamy su na mata dariyar keta,luu ta tafi zata fad’i da azama ya turo ciki tare da rukota.
“Deeja..
Gaba d’aya suka kallosu har Mamy jin kiran da Kamal d’in ke mata suka rufa kanta.
Jijjigata su ke,sai dai Deeja ba sauran numfashi.
“Mamy fa suma tai inaga..
Cicci6arta ya yi tare da d’aurata gadon Mamy Zaid ya tafi fridge dan d’akko ruwa sai ganan sun shigo shi da Abba a sukwane.
“Ku matsa,garin yaya ta suma?
Kauce wa sukai Abban ya hau gadon,yayyafawar ruwan duniya Deeja taki motsi dan haka dole su ka danganta da asibiti.
Yasan tai nisa a suman da tai dan likitoci sun tabbatar shock ne ya jawo mata haka anjima kad’an zata farfad’o.
Kowa yai jigum ana jiran tsammanin tashin Deeja.
Gida suka tafi jin numfashinta ya dawo normal amma sun mata allurar bacci.
Kamal ke kanta dasu Mamy a waje.
Ido ta fara juya wa da kok’arin zata bud’e su dan haka sai ya matso yadda in ta bud’e ta fara kallonshi.
Warai ta bud’e dan tuno da abinda ya faru dazun tare da kallon d’akin, akanshi idonta ya sauka.
Hannu ya dago mata halamun hi! Yana murmushi mugunta.
“Kin tashi?
Ido ta sa mishi tana mai tunano abinda da ya faru.
“Ba suma ba ai koh mutuwa ki ke kina dawo wa dole ki kar6i taimako na..
A zabure ta tashi daga kan pillown tana dafe kai jin komai ya dawo mata,a take ta fara yarfo mishi ruwan bala’i
“Wallahi Allah ya isa bazan ta6a yafe maka mugun kawai maketaci,dama wannan ne taimakon naka? Toh wallahi baka isa ba,dole ka sake ni..
Dariya ya fara irin wacce bata ma san ya iyata ba,dan irin ta ketar nan harda rike ciki.
Dan tsabar takaici kawai sai ta sau mishi kuka tana mai sake maimaita Allah ya isa ba iyaka yana dariya.
By
{SAFHA}..✍🏾
[4/4, 6:49 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFMA}
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
MMN HANEEP
4_Mamy ce ta shigo dan duba koh ta farka taji kukanta da Allah ya isan da take surfa ma Kamal.
Dariyar ya kunshe tare da gyara tsayuwa jin bud’e kofar.
Da harara Mamy ta bita,dan haka sai ta daina Allah ya isan ta hau kuka iya karfinta.
Fita yai ya basu guri, dan haka sai Mamyn ta sa mata ido cike da tuhuma.
“Kina nufin wai mijinki ki ke wa Allah ya isa?
Kukanta kawai take baji ba gani,dan haka kai kawai Mamyn ta jijjiga tare da fad’in
“Ya miki kyau.
Fita itama yi,ba daban kanta dake sarawa ba da ba abinda zai zaunarta asibitin nan.
Tare da likita su ka dawo sai harara take sau mishi,ganin haka yasa likita ya kalloshi tare da fad’in
“Mey aka mata ne?
Kallota ya yi duk yau d’aya ta fita a kamaninta.
“Ai da surutai ta tashi ne likita ni da na ma zata koh ta…
“A’a ka manta da hauka na tashi,mugu kawai,wallahi bullukututu dan bazan ta6a yafe maka ba har sai ka sakeni..
Kuka ta sake sawa baji ba gani dan haka ido kawai su ka sa mata.
Rokon Allah da annabi ta rika yiwa Abba akan auren nan ya raba in har yana sonta,ita a bata kowa ta yarda har Najib da dai a had’ata da Kamal.
Lallashinta ya rika yi da fad’in toh,tai hak’uri a koma gida sai ai batun,karshe sai da aka mata allurar bacci ta bar kowa ya sarara.
Washegari fur taki zaman asibitin a dole su ka sallameta,burinta kawai taje gida ayita ta kare.
****
Duk ta dawo kalar tausayi ganin babu sarki sai Allah,dan karan nan sosai Abba ya d’auke mata wuta,ga kyara gun Mamy,ga ketaka ta gun Kamal,bata da sauran dabara a yanzu dan koh Muneera Mamy ta dakatar ta da zuwa.
Kamar wanda aka tsikara ta mike zaune tare da kallon agogo.
Waya ta d’auka tare da danna kiran Najib.
Tsaki tai jin bai daga ba ta sake buga wa.
“Meye kuma?
Fuska ta marairaice kamar yana kallonta.
“Haba d’an uwana yanzu yau sati ina a bala’i amma koh ka kira balle kaji ya na kare?
Zurmashi ta rika yi kamar yadda tasan Najib kam akanta wawa ne har ya zirmu ya sakko.
“Yanzu ya ki ke so ayi toh?
Zama ta gyara tare da sanarshi taimakon da zai mata in dai har zata rabu da auren nan.
Gyale ta dakko tare da fito wa tana leke kamar munafuka, koma wa yai ganin tana sand’a lokacin da ya fito a kitchen da gorar ruwa a hannu.
Ruwan ya ajiye tare da binta ganin ta fice.
A tsaye suke ita da Najib din a bayan gida duk ya dawo wani soko a gabanta.
“A’a Najib,ka yarda dani karan nan in har ka taimakeni toh da wannan kaddarar auren gwara naka ka yarda da dan…
‘Yar dariyar da su ka ji a bayan su ne yasa tai shiru tare da juya wa.
Kallonsu yake had’i da dan jijjiga kai yana yar dariya jin yadda take raina wa Najib d’in hankali.
Harara ta sau mishi tare da juya wa ga Najib.
Murmushi Kamal din ya yi tare da kad’a kai,
“Bana tunanin na ta6a gamuwa dirinka ba sam Najib wanda karamar kwanyar mace ke badda tunaninshi 6at cikin lokaci kad’an..
Juyo wa sukai fuskar Najib din d’auke da mamaki.
“Mey ka ke nufi?
Deeja ya kallo tare yana murmushi,har mamaki yake yadda ta d’auki sa6a Allah a matsayin hanya mai 6ellewa a gareta,wannan mummunar dabi’ar tana d’aya daga cikin abinda yasa bai shiri da ita koh kad’an.
“Amma Deeja bakya tsoron Allah fa..
Ido ta zaro da sauri tare da bud’e baki.
Kai ya jijjiga.
“Da kina tsoron Allah da kin sanarshi cewa da kanki ki ka bada kwangilar rushe aureku saboda shima baya daga cikin burin ki wanda nasan shima yasan da haka..
Kallo Najib din ta danyi a sace,shima idon ya zuba mata kir dan gaskata gaskiyar lamari.
Sam bata iya karya ba musamman in an mata kamun kazar kuku irin haka,dan haka tuni ta hau mishi kame-kame yai saurin daga mata hannu.
“Ba ki da abin fad’i Malama, dan sai yanzu na sake tabbatar da ba karamin rainan tunani ki kai ba tun da..
Da sauri ta katseshi da fad’in
“Kadan ba karya bane..
“Dallah rufe min baki..
Baki sake take kallonshi da mamaki,wai yau ita Najib ke hantara bata da ta cewa.
“Wato bani da amfani sai in bukatar korar samarinki tazo koh?
Shiru tai ba bakin magana,dan haka tuni ya hau huce haushin shi kanta Kamal na gefe yana kallo jin yadda yake zazzageta gabanshi had’i da tonan silili.
Da kallo ta bishi baki sake har ya 6acewa ganinta ba bakin magana.
Kamal din ta kallo tamkar ta d’aura hannu bisa kai ta sau ihu koh ta shake shi ta huta.
Kafad’a ya daga mata tare da juya wa ya batta nan tsaye baki sake.
Koh ba komai ya toshe wannan 6arnar da ya jima tana kona ranshi ta tsakanin Najib da Deeja.
Ido ya rufe lokacin da yake tuno shan mintin nasu na karya da wai su ka d’auka abin dogwaro duk da su na cin nasara.
Abu d’aya su ka kasa gane wa,shine sa6on Allah sa6on Allah ne duk kuwa da K’ank’antar sa6on toh ya zama zunubi.
Iskar bak’inshi ya furzar tare da zama gefen katifa,fatanshi yasa daga wannan sun rabu kenan.
A fili ya furta zanyi maganinki!
*****
Ganin kunci yana neman hallaka ta yasata futowa falo inda take jiyo hirar su mariya da sauran yaran yan uwa da Abba ke rikon su, Sakina da Maryam sai Mariya datafi kowa kaudi a cikin su,.
Suna ganin ta suka saki murna don dama suna cikin damuwa ganin ta cikin kunci taki kula kowa sunai mata magana ta hausu da masifa, yanzu kuwa da suka ganta cikin walwala har rige-rige rikota sukai cike da murna suna karai mata sannu da jiki,
Nan ta sake cikin su suna hira shakiyancinsu harya fara batar mata da damuwar ta, Mamy data leko ta gansu haka saita bisu da murmushi taji dadin ganin yanda tasoma sakin jiki sakamakon kwanakin baya da take yini a d’aki cike da kunci da damuwa.
Shigowar sa falon ce sanadin dakushewar farin cikin ta,
Shikuwa ko kallon inda take baiba illah sabon darasin hira da suka bud’e da yaran yawan cin hirar tasu akan ‘yan matan yanzu ne, jin an tab’o inda ke masa k’aik’ayi yasashi gyara zama don ganin yasamu damar goga mata zana.,
Saida yakai lomar Abinci bakin sa” kuna jina? Wasu fa ‘yan matan na yanzu ba gwara garin kwaki da suba, a arha b’agas ake tafiya dasu kuni wacce igiyar soyayyata ta zargomin ko naira hamsin kabata kana iya sumbatar kuncin ta ko fiye da haka ke alakoro ma inta yaba murmushin ka saita baka ka tsotsa”,
Dif! Sukai danjin yanda akalar zancen nasa ya dosa duk da basu fahimci ainihin meyake nufi ba sunsan dai da Deeja yake, don haka sukai kallon kallo a tsakanin su sukai dariya tareda canja akalar zancen.
Deeja kuwa? Jitai marar ta takulle hankalin ta yatashi shikad’ai yajiyo sautin da cikin ta yabada kullllll!! Alamun tsurewa da batun sa,
Don haka ya gumtse dariya ganin duk ta firgice tayi narai- narai da ido tamkar tasaki kuka don tasan Kamal zai iya tona asirinta gurin k’annan ta don kirki bai isheshi ba,
Duk da ya kunshe dariyar sa saida takai da kubucewa don ganin tamike tsam tana b’arin shigewa band’aki da gudu.
*****
Cikin wannan kwanaki ya hana kansa sukuni a sakamakon abinda yayi mata rannan a gaban su Sakina, don haka yafaki idon mamy dake kicin ya fad’a mata d’aki ya maida kofa yarufe.,
Zunbur tamike a razane don bata tab’a tsammatar zai bankado mata d’aki cikin irin wannan lokacin.,
Ganin ta taso masa yasashi dakatar da ita,
“Kinga karki tareni da hayagaga Abu d’aya zuwa biyu yakawoni gareki,
Yafara magana cikin tausasa murya.,
“Na farko naga kwana biyu kina boye kanki a d’aki bayan naga rannan kece harda zaman hira a falo shine nazo naji ko lafiya?
” sannan kuma intayaki jajen Abinda yafaru”,
Shuru yai yana saurarar cewar ta,
Shuru ta shareshi, ya tsira mata ido da kyau yana nazarin ta, ta rame sosai damuwarta na tasowa ne tun daga tsakiyar zuciyar ta a lurar da yayi mata kenan, yajima bai mata irin wannan kallon kurillar ba yanzu sai yaji miliyoyin sonta na tasomasa muryar ta kawai yake da muradin ji gashi kuma taki magana,,
Ya sake gyara tsayuwa yanai mata dariyar tura haushi,,
“Au na manta naga kwana biyu kun bata da me debe miki kewa ni kuma dazan debe miki ta ainihin kin nunan iyaka ta”
A kufule tace”
“Burinka yacika to yanzuma zaman nan da nake ubangiji nake kaiwa k’rarka kuma gashi tun ba’aje ko inaba yasomai min sakayya”
“Amma yakamata ace cikin kunya kikayi maganar nan”
Duban rashin fahimta taimasa,,
“Yanzu duk rashin tsarkin ki bakiji kunyar gurfana gabansa kina kai karar mutumin kirki irina? Ko bakya tuna abinda kukai da Najib?
Ta kasa magana,,
“Da kinada hankali da tunani jinjina ya kamata kimin dana taimake ki na aure ki donni naganki yakai sau dari a yanayin dabai dace ba tare da Najib,,
“Amma bantaba fasa sonki ba Deeja, kinga shi Aminu gani d’aya yayi miki kuna asha ruwan tsintsaye ya zargawa Karen sa igiya to kice da yaga Najib sakale da kugun ki yana kokarin zira miki harshe a baki had’iyar zuciya zaiyi ya mutu”
Ba shiri tamik’e zaune cikin haki tana waige-waigen don tsoron kar wani yajiyo su,,
Kamar zata rushe da kuka tace” kai Kamal kaji tsoron Allah yaushe kaga Najib sakale da k’uguna?
“Kina nufin sak’ale k’ugu baikai tsoma harshe cikin baki bane?to ai naga abinda yafi haka ma kuma ko agaban wanene zan bada shaida”
Kofa tanuna masa cikin tunzura, “tafi bayan duniya kabada shaida”
“Aiba saikin sani ba ko rakiya kika gayyace ni lokacin da kuke sheka ayar ku?.
“Ni yanzu Alfarma nazo nema tunda Najib yagudu nasan kina cikin damuwa don haka ki taimaka kibani dama na maye gurbin Najib duk Abinda kike zaton ya iya dama wanda kike bukata babu wanda ban iyaba har karima sai kinsamu”.
Hawaye tasoma tana marmasa ido tsoro fal ranta,
“Kamal Dan Allah kafuta kabani guri inhar ka gwada kanason tarewar mu Allah ya isa ban yafe ba haka inka kuma shigo min d’aki,,
Yana dariya ya amsa,,
“Allah ya isar shigowa daki kawai zan guda amma maganar tariya banida matsala inhar zan dinga zagayowa koke ki faki ido kuzo tomu shekara a hakan”
Zuwa yanzu tafara kuka wiwi,
Duk da yalura kamar numfashin ta zai dauke don kuka da tashin hankali amma bai fasaba,,
Yanzu nazo kinsame ni a b’agas haka zaki barni natafi a bagas? Kibani dama ko d’aya ce Najib bazai nunamin iya shan minti ba donni ma ba baya bane”
Tariga tagama kaiwa karshe don haka ta d’ora hannu a ka ta kwarma uban ihu, tuni kamal ya b’ace,,
Mamy da Abba ne sukai rige rigen shigowa suga wanne hali ‘yarsu tashiga data cika gidan da wannan uban ihun…..,
Tsaki mamy tasaki tai komawar ta kicin cike da takaicin khadeeja,
Shima Abba rufeta dafada yayi kana ya futa yana fadin nasan ”
matakin da zan dauka akanki”
****
SAFMA
[4/4, 6:49 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).
5_Ba koh sallama aka bankad’o kofar d’akin nasu sai huci take kamar ta ci babu.
Ido ya sa mata fuskarshi ba yabo ba fallasa,har mamakin zuciyarshi yake in ya tuno wai tana kwadaituwa da son Deeja.
Yarinya da ciwan kanta ma a ganinshi bata sani ba balle tasan na wani.
Ya sani a in da wanda Deeja taki jinin gani a yanzu toh bai wuce shi ba,dan tana mishi tsanar da k’arara kowa ke iya ganinta kwance bisa fuskanta.
Murmushi ya yi a zuciyarshi, abu daya ne bata sani ba,aurenshi da ita shi ake kira *Mutu ka raba, wai takalmin kaza*.
***
Fushi ta diba yi da kowa cikin gidan har Abba,dan ya sake jaddada mata hukuncin shi na nan bisa kanta.
Ba ruwanta da sha’anin kowa,kamar yadda kowa ya d’auke mata wuta,abinci sai ta ga dama zata ci.
Kusan wata guda kenan da auren,dan haka Abba ya ce su tattara a tare haka nan kila in ta bar gida zata saduda.
Ranar taci kuka jin da gaske zata tare gidan Kamal.
Kamal d’in ne ya samu Abba da zancen kaita garin su.
“Abba ina son muje chan Kogar gun Abba kamin..
Kai ya dan sosa yana sinke kai,dan haka sai Abban ya kad’a kai yana murmushi.
“Ai munyi waya na sanarshi komai,dan haka ka tafi da iyalin naka chan dan su santa.
Kai ya sake duk’arwa yana godiya.
Deejan ya kwad’a ma kira,chan ciki ta amsa tare da fito wa tana chunno baki a dole ita fushi take dashi.
“Ki kimtsa za ki bi mijinki ya nuna miki ‘yan uwa kamin ku tare chan Kogar da sauran su.
Kai ta dago da sauri tana kallon Abban kamar ta sau kuka,dan haka sai Kamal din ya basu waje.
“Khadija..
Nan a ciki ta amsa.
“Na baki dukkanin wani so da kulawa,ban ta6a neman wata alfarma a gareki ba sai wannan.
“Ki min alfarmar yi wa aurenki biyayya,kar ki bani kunya in kunje gun abokina koh danginshi..
Jinshi take kawai har ya gama,ita tunaninta ya ma zata iya rayuwa cikin kauyen su Kamal koh ta yini ne,dan haka ba komai taji ba illa tunanin abinda zata riska.
***
A Kogar.
Kallon kowa take a raine, duk da su sun mata tar6ar kirki da karamci barin su Badiyya k’anwar Kamal.
Duk ido ya sa mata yana karantar ta,hatta abinci taki ci sai yatsine fuska take halamun ta raina muhallinsu.
Tunani take yanzu kila wannan matar har ita auren Baban Kamal ya kusa sittin..
Kai ta girgiza,
“A’a na barshi a talatin..
Nutsuwa tai tare da kallon ko’ina, d’aki ne na kasa yasha leda sabuwa ko’ina kal-kal.
Baki ta dan ta6e,duk yana kallonta ta window.
Kai ya jijjiga tare da shiga d’akin.
Rai tai saurin had’ewa tare da mike wa.
“Na fa sanar ka ni ban son shisshigi ka rika yin nesa-nesa dani da inda nake.
A raine yake kallonta, chan dai ya jijjiga kai tare da fad’in
“Ki shirya gobe riga zamu dama,da sannu zan karad’e miki kauye nah kamar yadda Abba ya ce.
Harara ta maka mishi,sai ya jijjiga kai ya fuce.
***
Kwanan su d’aya a Babban gida washegari ranar kasuwa ya samu ‘yan uwan Mamanshi sunzo cin kasuwa dan haka tare zasu bisu.
Ido ta zaro ganin motar da ake d’anewa wai nan zata hau.
Da hannu ta nuno mishi motar.
“Wai kana nufin a wannan akori kurar motar zamu tafi?
Kai ya d’auke tare da sanya jakar su,
“Malam da fa kai nake..
“Ki jira sai na miki bayani.
Motar ya d’ane kamar yadda yaga sauran sunyi ya batta baki sake tana sake karewa buddadiyar motar kallo.
Masifa ta fara a kan fafur sai ya sauke mata kayanta dan fa ba ta6a hawa ba,ba kuma zata hau ba.
Kai ya jijjiga
“Toh ki san inda dare ya miki tun wuri..
Harara ta galla mishi tare da rike k’ugu tana masifar dole ne sai taje?.
Jin mota na dirin tashi ga wasu gunguma gunguman shanu na taho wa yasa ta fara raba ido.
Banza yai mata har aka tada mota,
“Toh ta ina zan hau?
Juyo wa yai tare da kallonta,kan ta aune har ya sau dariya.
Dakyar ta iya hawa shima sai da ya taimaka mata.
Tafiya akai mai d’an nisa tana gani ya tushe rabin fuskarshi.
Sosai yau ta jigata, harda kukanta lokacin da za a sauka taga wai ba’a zo ba an tsayarda babur wai mota bata shiga wajen.
Haka tana ji tana gani ta d’ane babur ga magriba ta sanyo kai sai dariyar keta yake mata.
Duhu cur suka isa rigar Mongwano,ga bakar yunwa,ga gajiya,tun kan aje ko’ina har ta tantance Kogar babban birni akan nan ganin yadda take cin karo da bukka.
Cikin yaren fillanci suka kewaye su da fitulu cike da murnar zuwan Kamalu.
A jigace ta kalloshi,
“Ruwa..
Ido ya sa mata,tun kan aje ko’ina har ta shiga hankalinta.
A ‘yar karamar kwarya aka kawo mata ruwan dan haka kawai sai ta daga ta hau kwankwad’a.
Tasha kusan rabi taji ina ba gama ga wani karni da ruwan yake.
Sauke wa tai tare da haska shi.
Gaba d’aya bai mata kalar ruwa ba,yafi kama da lamurje,dan haka da sauri ta ajiye tare da fara yatsine fuska kamar tai amai.
Kai ya jijjiga, yana auna bata ma ga komai ba..
Abinci kuwa loma d’aya ta cire hannu tana kallonshi yadda yake shan nono.
Harara ta galla mishi tare itama d’auka ta ture abincin.
Kur6a d’aya tai saurin furzarwa jin tai karo da tsami da wani dogon abu.
Nonon ta haska,sam ba irin na gari bane duk ba kyan gani.
A marairaice ta kalloshi jin yadda yake sakar dariyar keta.
“Amma dai dama kashe ni kazo yi garin nan koh?
A dirare ya kallota ba kiftawa,kan ta farga ya sake ke cewa da dariya.
“Welcome to Mongwano city..
Kuka ta saka mishi cike da jigata ga yunwa.
“Yarinya baki ga komai ba ma,a gaba akwai inda zamu koh wannan din ma ba zaki samu ba..
Baki ta ta6e tana mai sake artayo kukanta har mutanen gidan su ka fito ganin koh lafiya.
Lalle yau ta sake yadda da bakar muguntar Kamal mai yawa ce.
Da fillanci yai musu magana,dan haka sai d’aya ya koma tare da dakko mata kosai da fanken da ya siyo a kasuwar Babban guda ya bata su na mata dariya da fulanci.
Dama-dama, dan haka tana ji tana gani wannan taci yana ta kela mata dariyar mugunta.
Gado aka bata a cikin ‘yar dukurkurar bukkar wanda sai ta tsuguna take tsayuwa.
Ajiyar zuciya ta sau tare da kallon ‘yan matan dake gulmarta su na kunshe dariya.
Kaya ta cire tare da sanya na bacci ta daura zani a kai.
Zani ta sake shimfida wa bisa gadon jin yadda yake sukarta tamkar da kaya akayi shi.
Chan taji abu na dan zubo mata bayan ta kwanta.
Waya ta haska tana tsaki a zatonta koh kasa ce.
Wasu k’ananan kwari ne da gara ashe da wasu bak’ak’e suke zubo wa daga sama.
Baki ta ta6e da zummar sakar kuka dan bakin ciki,ina wai Kamal ya kawo ta?
Gyalenta ta dakko tare da lullu6a tana tsaki ita kad’ai tare da kallo y’an matan da suka kwanta abin su.
Abu taji yana yawo bisa kanta a saman gyalen,dan haka tuni ta fara raba ido tare da janyo waya a hankali.
Gyalen ta yaye tare da haska wa,wata bakar katuwar kunama ce ta daga kari sama,da karfi ta yar da gyalen tare da dira a gadon ta ari na kare ta fuce tana ihu
“Wayyo kunama…
Tashi yai tare da saurin zuwa inda take kukan,tana ganinshi ta rukunkumeshi tare da fad’in
“Wallahi bazan kwanta a d’akin nan ba..
Mutanen gidan ne suka fito jin ihun nata.
Hannu ya kai kan bak’inshi yana fad’in
“Shshhh,to anji, bata cije ki bade koh?
Kai ta daga da sauri tana maida numfashi.
Fur taki koma wa,karshe inda ya kwanta da Buba nan ya ra6a mata ta raka6e daga zaune shi kuma ya shige makwancinshi.
Yadda take rike da hannunshi kam yasa ya sa mata ido,yau d’aya har ta dawo abin tausayi.
“Ki ma ware,dan sati muka zo yi a nan.
Ido ta zaro tare da marairaice fuska,da sauri ta hau burburwa fad’i take
“Wallahi baka isa ba gobe zan bar garin nan.
Kai ya girgiza tare da fad’in
“Toh mu zuba,ai sai randa naga kinyi ladab.
Ranar kam tasha kuka da kiran Mamy,tasan in tai sati a garin nan kila sai dai a d’au gawarta.
Karyar raina mishi muhalli yasan ta kare.
By
SAFHA..✍🏾
[4/4, 6:50 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).
6_Da asuba ta farka,duk da dama baccin rabi da rabi tayi tana tashi yin dube-dube na dangin kunama,ga duk ya cinye wajen kad’an ta samu ya bar mata ta ra6a.
Juyi yake shirin yi duk wuyanshi ya k’age da kwanciya gu d’aya.
Ido ya sa mata ganin yadda zauna tare da sanya kanta bisa kafafunta a haka take bacci.
Tausayi ta bashi ba kad’an ba,dan yasan tabbas ba tai wani baccin arziki ba yau.
Dan haka hannu ya kai da niyar kwantar ta kwala ihu tana raba ido.
Harara ya sau mata tare da fad’in
“Wai ke abin ihu bai miki kad’an ne?..
Da sauri ta ce
“Eh d’in..
Kai ya jijjiga tare da tashi tai zirif ta mike.
“Ina zaka?
Banza yai mata tare da d’aukan buta sai ta bishi tana wai waye.
“Mey ki ke nufi ne wai?
Rai ta had’e tare da fad’in
“Abinda ka ke nufi,kana nufin ni kad’ai zaka bari a kurumin dajin nan?
Ido ya sa mata,karshe sai koma wa yai sai da gari yai sha ta barshi yai alwala.
A kan su ta tsaya ana tatsar nono ‘yan mata sai kwankwad’a suke,fuska ta hau yatsine wa tamkar tai amai yana kallonta yana jijjiga kai.
Karshe itama sai wannan d’in tasha,dan fa biskin jiya aka sake kawo wa wai dashi za ai break.
Deeja kam taga rayuwa,wacce take ga in ta kara kwana uku tabbas sai dai a d’au gawarta.
Rafi ta raka ‘yan matan rike da abin diban ruwa.
Ido tai saurin zaro wa ganin ruwan da zasu dina ga nan shanu sunyi layi su na sha,su na k’auce wa karnuka su ka hau layi.
K’ak’arin amai ta fara tuno da jiya tasha ya kai rabi,dan takaici har da kukanta ‘yan matan na mata dariya.
Su na dawo wa ta tubure mishi ita fa sai an tafi sam shi kam yaki kula ta.
‘Yan matan ya tambaya sai su ka mayar mishi abinda ya sata kukan,wai akwai rijiyar dad’i tai hak’uri an jima za su je su debo mata sai dai da nisa ne.
Rayuwa kam Deeja ta ganta a rigar Mangwano,shi da kanshi daurewa kawai yake,kwanan su hud’u sukai haramar tafiya.
Daga wannan lokaci bata sake tanka mazauninshi ba koh kiran shi da d’an kauye,dan ya sanarta akwai rigar da tafi wannan, chan zasu.
Da harara kawai ta bishi,dan tasan tsaf zai aikata,mugu kawai.
Koh sati basu fi ba su ka tare a gidan hayar da ya kama kamin ya idda gininshi.
Ranar ansha kuka,sai dai fur iyayen su ka ce zamansu kam a nan ya k’are,haka tana ji tana gani aka tasa keyarta gidan Kamal.
****
“Bana jin zan ta6a yafe maka dan kai sanadin da duk wani hangena ya rushe.
“Ka sani *INA DA BURI*, amma ba irin wannan ba..
Baki ya ta6e yana gyara kwalar rigarshi.
“Chan ta matse miki kuma wannan, dan yanzu babban burinki ki san hanyar faranta min in har kina so na daga k’afa..
Harara ta sau mishi tare da fad’in
“Allah sauka min ni Deeja,ai yadda kai sanadin komai,dole komai ya shafe ka..
Murmushi ya yi tare da jijjiga kai tare da daga kafad’a ya fuce.
Da yamma Muneera tazo kawarta,
“Iyanzu kam ya kamata ki ajiye makaman yakin ki Deeja,ina gudan miki ranar da zaki kasance baki a tsuntsu baki a tarko,ki yarda ke ce ke da mukulin saita duk wani Burinki ya koma yadda ki ke so,dan za ki iya saita tunanin namiji ta yadda ba kya tsammani..
Baki ta ta6e halamun abin bai ahigeta ba.
“Muna nan da ke da sannu cikin ruwan sanyi sai Kamal ya gane bai da wayo..
Hannunta ta riko.
“Yanzu yana a matsayin mijinki ne,dole ki bishi in dai kina son ki tsira gurin Allah..
Hannun ta zame tare da fad’in
“Toh uztaza,mu bar wannan layin kawai..
Kai Muneeran ta jijjiga, tasan kawarta kam tai nisa, zai wuya taji kira cikin sauki.
Har ya dawo su na nan tare kamin tai musu sallama ta tafi.
Da harara ta bishi bayan ta dawo a rakiya ya bita da kallo,kai ya jijjiga,ya kusa saita tunaninta lalle.
Kimanin sati biyu kenan da tarewar su amma kullum sake 6otsare mishi take da wani salon.
Da dare ya yi zata sakace d’akinta sai dai yai kwanan parlour.
Abinci sai dai ya dafawa kanshi,yau dai ya kudiri aniyar saita wasu abubuwan,dan haka ya ce
“Ina abinci na?
Sama da kasa ta kalleshi a wulakance tana shafa mai
“Kai da wa?
Ido ya sa mata sam bai da walwala yau,dan haka a tunzure ya shige ciki tuni ta mike tsaye.
“Nai miki hak’urin sati biyu da kawaici ba kya gani koh?
Rai ta had’e da sauri ganin ya karaso tai band’aki da sauri ta datse tare da fad’in
“An fad’a baza’a dafa ba d’in.
Yin duniya taki ta bud’e, karshe
kamar kullum yau ma shi ya dafa.
Da daddare ta gama shirin kwanciya kamar kullum ta tashi zata rufe kofa ya danno kai.
Rai ta had’e da sauri had’i da rike k’ugu.
“Lafiya?
Juya wa yai tare da maida kofa ya rufe had’i da cire mukulli ya juyo yana kallonta.
Cike da in ina ta fara fad’in
“Na..na..ce lafiya?
Hannun riga ya fara tattare wa yana murmushin mugunta.
“Ki bari ai zan nuna miki koma meye..
Baya ta fara ja tana had’iye yawu kwat tana raba ido.
Kanta ya yi dan haka da sauri su ka fara ‘yar tsere cikin d’akin, fad’i yake
“Yau zan maganin ki,dan ni kad’ai zan iya miki kin sani,wannan fitsarar yau zata tafi garin su..
“Ba haka mukai da kai ba,bana ciki da mugunta…
Shiru tai ganin ya damko ta da duk karfinshi,tuni ta fara kukuwar kwace wa tana masifa.
“Wannan ai iskanci ne..
“A gunki na gani ai na koya..
Magana zatai yai saurin toshe mata bakin ta hau mutsu-mutsu, tun tanai har tai lakwas,dan haka da sauri ya janye kanshi su na maida numfashi.
Yawun bakin ta tattaro tare da tofarwa tana goge bak’in.
“Mugu kawai…
Murmushin mugunta yai tare da jijjiga kai
“Ke kuma munafuka ba,ai gwara ma ki shanye,tun dama abin neman ki ne ya samu,a kuma yau mai gaba d’ayan zai zo..
Matsa wa tai tare da nuno mishi kofa.
“Ka fitar min a d’aki malam..
“Kin biya kud’i ne da ya zama na naki?
Matso wa ya fara tana ja da baya,sosai yau kam ta gano ketar ce ta motsa,in kuma batai da gaske ba haka zai shata a banza, dan haka da sauri ta dawo sabuwar masifa.
Muje zuwa
SAFHA…..✍🏻
[4/4, 6:50 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP)
7_ Pillow ta fara hullo mishi tare da d’ane gadon ta tsaya,duk huci suke ganin yadda sukai ta tsere tana zille wa.
“Dama kin bar wahalar da kanki,dan kinji na rantse yau saina seta tunaninkin nan..
“Ka fara saita naka,amma ba dai nawa ba..
Tsalle ta doka da niyar sauka a gadon ganin ya kawo mata raruma ta gurd’e,duk da haka da karfin hali tai hanyar kofa tana cije le6e ya cimmata kamar wasu yara.
Tamkar masu tseren gaske haka suke sauke ajiyar zuciya ya gamata da kofar d’akin.
Ido ta tamke kam ganin yana niyar gama fuskar su ta fara tuttureshi.
“Wane irin mugu ne wai kai?
Murmushi ya yi yana kallon bakin tsiwar.
“Ki tsaya ki amsa da hankali..
“Bana so.. Allah tsare ni ka do6an baki.
Yin duniya ta kasa kwatar kanta,dan haka batai wata-wata ba ta gartsa mishi cizo a hannu iya karfinta da ba shiri ya sauta.
Da dingishi ta nufi hanyar band’aki tana mako mishi harara tare da yarfe hannu jin zugin kafarta.
Kai ya jijjiga shima yana yarfe inda ta cije shi, yau kam wallahi yaso koya mata darasi amma taci sa’a ba wai dan bazai iya kamota ba ta karfi.
“Gobe in na ce ki min girki ki kiyi ki ga yadda zamu karke dake..
Harara ta maka mishi ganin yana bud’e kofar zai fita.
Ajiyar zuciya ta saka tare da dafe kirji.
“Mugu kawai,cizo yai rana.
****
Kitchen take tana dafa indomie da zata ci, ta tsinkayo muryar Zainab mak’ociyarta dake shigowa gidan wasu lokutta. Falon ta fita suka gaisa ta kar6i y’arta Ihsan tana mata wasa.
“Ya naji gidan shiru, ko maigidan baya nan ne?”.
Yatsine fuska ta fara yi kana ta bata amsa da cewa’ “ya fita, yo ma ko yana gidan me zai k’ullata min ne daya wuce takura”.
Murmushi Zainab ta yi tana mai mamakin halayya irin ta Khadeeja, saboda d’an shigowarda take yi ta fahimci cewa akwai takun sak’a tsakaninta da Kamal.
“Gaskiya Khadeeja ni ko ina hango wautarki a wani 6angaren”.
Kallo ta bita dashi mai alamar tambaya, cikin halin ko in kula ta furta’ “wauta fa kika ce Maman Ihsan?, kamar yaya?”. Ta furta hakan tana mai wasa da kalabarda ke saman kan Ihsan.
“Wauta mana, saboda in ba wauta ba mai sankacecen Miji kamar Kamal har zai yi mai rik’on sakainar kashi, kar ki manta yanda tsadaddin Maza suke wuya a wannan lokacin”.
Dariya ta kece da ita har da ubar k’wallarta, saboda yanda maganar ta bata dariya, wai sankacecen Miji, “Kamal baya gabana, saboda INADA BURIN da ba lallai ne Kamal ya iya cikamin shi ba”.
Bud’ar bakin Zainab za tayi magana kenan ta tsinkayo muryar Kamal taja bakinta ta tsuke, nan ta kar6i Ihsan daga hannunta had’e da furta’ “ni zan wuce sai wani lokaci in kin samu lek’o gidan namu”.
A k’ofar shigowa ne suka ci karo dashi ta rakota, nan ya ra6e ya basu hanya suka fice shi ko ya k’arasa daga ciki.
K’amshin girkin da ta d’ora ne ya ja hankalinshi ya fad’a kitchen d’in. Ganin k’aramar tukunya akai ya bashi tabbacin ko miye take girkawa ba dashi take girka shi ba, kuma gashi ya kwaso yunwa da zafin rana.
Filet ya d’auko ya juye indomie d’in ya d’auka ya shige d’aki har da murd’a key, sai da ya rage kayan jikinshi sannan ya yi zaune ya fara kai loma.
****
Baki ne ta saki saboda hango y’ar k’aramar tukunyar da ta d’ora ajiye a gefe, wanda ke nuna an juyen abincin. Dakin kawai ta tunkara ta murd’a k’ofa ta jita a rufe, ji ta yi tamkar ta kurma ihu saboda tabbacin Kamal ne ya juye mata indomie ya shige d’aki yana ci.
“Wallahi ka bud’e k’ofar ka bani abincina, in ba zalunci ba haka kawai za ka zo ka tararda na yi girkina ka juye, hala ni baiwarka ce, ko kuma an kawo ni gidan ne domin in yima girki?”. Masifa take yi tana bugun k’ofar tamkar za ta 6allata.
Yanda kasan bebe haka ya koma mata, sai da ya cinye abincin tass sannan ya fad’a toilet ya yo wanka ya fito ya kimtsa cikin k’ananan kaya sannan ya bud’e d’akin ya fice.
****
Wata indomie ce take dafawa ta yi tsaye tana gadin abarta sai cizon yatsa take yi tana huci tamkar wata kasa.
Cikin sand’a ya k’arasa kitchen d’in wanda dama ta jiyo k’amshin turarenshi, tana batun juyawa ta balbaleshi da masifa taji ya sagalo hannunwanshi duka biyun ya rik’e k’ugunta had’e da kwantar da kanshi saman kafad’arta.
“Yanzu don kin girkawa mijinki abinci ya ci shine abin masifa, ya kamata fa yarinya ki bada kai bori ya hau, saboda nasan kinyi kewar wannan”.
Yana gama fad’a ya juyo da kanta saitin fuskarshi. Baki ta bud’e da niyyar masifa karaf ya had’e bakinsu guri d’aya yana juya halshenshi cikin bakinta, jin cewa jikinta ya saki gaba d’aya ya sake ta had’e da ja baya, sai gashi ta fad’o mai saman jiki.
“Haba Yarinya, karki cemin d’an wannan abin yasa kin kasa d’aukar kanki, wannan ai shafar mai ne”.
Cikin borin kunya ta fizge jikinta daga gareshi ta yi mai wani mugun kallo, sannan ta juye abincinta ta bankad’eshi ta fice inda ya bita da dariyar k’eta.
Muje zuwa
Daga Alk’alamin (SAFHA)….✍🏻
[4/4, 6:50 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).
*_Naki ne wannan, our dorling Dota Feedoh,(‘Yar Fichika)..saura 4😹*_
8_”A’a, Aunty amarya ce a gidan namu?
Murmushi tai tana d’aukan Ihsan.
Bayan sun gaisa ta d’au littafin da ta gani bisa kujerar Maman Ihsan na hausa tana duba wa,sosai ta nutsu cikin shi sai murmushi take ita kad’ai.
Kai Maman Ihsan din ta girgiza mata tana murmushi tare da ajiye mata plate din hannunta mai d’auke da ruwa.
“Haba,haba Malam,ki duba irin wannan soyayya da ake shinfid’awa a littafin nan exactly irin wacce nake da *Buri*.
Littafin ta ajiye tare da ta6e baki da marairaice fuska,
“Bana tunanin mugun nan zai iya rabinta,dan har gwara ma gidahuman chan su Aminu dashi…
Shiru tai ganin yadda Maman Ihsan din ta sau baki tana kallonta.
“Na tambaye ki man Deeja?
Kai ta jijjiga halamun tana ji.
“A yadda na fuskanta ke burinki a soyayya ya k’are,ba ruwan ki da sauran burin gidan aure sai wannan koh?
Kai ta daga mata da sauri.
“Sosai kuwa,dan ni fa akan wannan burin nawa bansan adadin samarin da na fatattaka ba,sai gashi yanzu wannan mugun a araha ya sameni sidan..
Ido ta sa mata,
“Amma kuna da alaka da Kamal?
Kai ta girgiza da sauri.
“Bamu da wata alaka sai ta nesa.
Murmushi tai ganin yadda take yatsine fuska.
“Amma zan so jin tarihin ku da yadda wannan auran ya kullu Deeja,kin san har yau mamakin ku nake wallahi.
Baki ta ta6e tare da gyara zama.
“Kamal fa mu karu yake zaune a gidan mu,Abban mu ne ya rike shi tun zamanin yana shekara 10 yazo Kano,Baban shi abokin Abban ne,sai shegen auri sakin bala’i kin san dai mutumin kauye..
“Tare toh su ka taso da yayuna maza dan ni kad’ai ce mace sai yaran riko yanzu gun Mamy.
“Allah ya gani tun tashina jini na bai ta6a gamuwa da shi,gashi shi yafi kowa sanin wani halina da koh a gida basu sani ba,dan fa kusan duk a idonshi ya wakana..
Shiru tai jin ta kwafsa,dan haka cike da halamar tambaya Maman Ihsan ke kallonta,ya ta iya,ta riga da tayi subutar baki.
“Ban sanki ba,sai had’uwar makotaka, haka kawai naji na aminta dake,shi yasa ma ban boye miki zaman mu ba,dan wallahi ni bana sonshi..
Ido Maman Ihsan din ta zaro,
“Toh wa ki ke so?
Ita ma idon ta sa mata,kamin daga bisani ta girgiza kai.
“Ba kowa,abu d’aya na sani shine *INA DA BURI*,burin da har yau ni banga wanda zai iya cika shi ba…
“Dan tsaya dan Allah..
Shiru tai tana kallon Zee din,
“Meye burin naki? Dan Allah ki sanar ni..
Murmushi tayi tare da sake muskutawa.
“Burina nai auren soyayya,irin soyayyar da nake gani a India da littafan soyayya..
“Irin soyayyar da mijina zai ji ina ma ya bani ranshi dan so..
“Irin soyayyar da kullum zan rika jina a sama,ya zamana ni dai d’an soyayya na aura.
Yadda komai ya wakana ta sanar mata har zuwa aurenta da Kamal da yadda aka fasa da Najib.
Ajiyar zuciya tai tare da furzar da iska tana marairaice fuska.
“Sai dai fa ban samu abinda nake son ba,dan kusan duk samarin da nai kidahumai ne,ba abinda su ka iya sai bud’e hakori,da naga ba haza zan ma kora da hali,in ka ki abu d’aya zanyi wanda koh a hanya ka ganni bani ba kai..
Zama Maman Ihsan ta gyara,
“Wani abu ne wannan? Allah yasa ba abinda nake tunani bane..
Da ido su ka kafe juna,ita kanta tana kunyar tuno da wautar da ta shuka ita da Najib dan kawai bukatar ranta.
Kai ta sunkuyar tana murza yatsa.
“Ina jin ki..
Kasa ta kara yi da kai tare da fad’in
“Soyayyar minti ne muke yi ni da Najib cousin na,wannan ce kawai in nayi nake rabuwa dasu a cikin ruwan sanyi,toh shine,shine fa…
Shiru tai sake yi tana dan sosa keya ganin yadda zee din ta kafeta da ido.
“Ni fa har ga Allah Maman Ihsan ta karya muke yi,amma Kamal da yasha kamamu yaki yarda a hakan,shine kullum sai nasha gori gunshi..
Kasa tai da kanta tana chunno baki.
Ajiyar zuciya Maman Ihsan din tayi.
“Tab,lalle wannan shine kwamachalar..
Kallota ta danyi da halamun tambaya, dan haka sai ta gyara zama.
“Gaskiya kinyi shirme, babba kuwa..
“Sannan ki gode Allah da Kamal din ya taimake ki baki auri Najib ba shi ya aureki..
Kai ta dago da sauri tare da sakar baki,dan haka sai ta kad’a mata kai.
“Kwarai kuwa,koh kina tunanin duk abinda ku ka shuka ba zaki girbe ba a gaba?
Kir ta kafeta da ido,dan haka sai ta cigaba.
“A fa gareki ne abinda ki kai ki ka d’auka a wasa,amma ga samarinki da kuma Allahnki ba wasa bane,dan Najib ba muharamminki bane,koh hannu ya rike miki zunubi ne babba balle azo ga su runguma..
Kai ta sake sunkuyar wa halamun ta gamsu.
“Ita rayuwar nan yanzu da ki ke kallonta wallahi Deeja samari kiris suke jira ki samu tabo,dan fa ko wani saurayin ne yazo a barshi a kin samu dai dai ke,shin bakya tunanin wani yazo ya fad’i halinki wanda a shine silar rabuwar ku?
Shiru tai mata halamun ba gaskiya.
“Dan haka ni a gani na Kamal taimako yai miki da bai barki da Najib ba dan fa a tsakanin ki dashi ba wani sauran mutunci dan ya gama gogar ki da shafar ki a sunan mafita.
Sosai tai mata fad’a, kuma ta gane kuranta har tai istigifari.
Abu d’aya ne bata yarda ba wai Kamal taimako yai mata,abu d’aya ta sani ya taimake ta ne dan ya taimaki kanshi,dan tafi kowa sanin ketar Kamal da bakar muguntar shi.
Sallama sukai ta fito,a bakin kofa ta tararshi ya bake hanya.
Kallon sama da kasa ta mai ta kautar da kai.
“Da izinin wa ki ka fita?
A yatsine ta kalloshi,
“Ji wani karfin hali,toh kai a wa?
Ido ya sa mata,ya ma rasa amsar bata,dan haka kawai sai ya wuce ciki ta bishi da harara.
Sosai ta kunnoshi,dan haka da yaje d’aukan pillow ya tsaya bisa kanta.
“Ya zama rana ta karshe da zaki sake fita ba tare da izini na ba dama..
Kallon tara saura kwata ta fara mishi,a haka ya iya kama kai da iya fad’a, amma a soyayya an baro shi baya…
“Mtsww..
Tsaki ta sau mishi tare da mike wa ta zauna.
“Ka fa daina d’aukar kanka a matsayin miji, wallahi darajar Abba kad’ai ke zaunar ni,da kai baka isa ba wallahi..
Kanshi ya nuno da hannu tare da fad’in
“Ni ki ke wa tsaki?
Da sauri ta ce
“Eh din,dan baka isa ba..
Jim yai yana kallonta baki sake.
“Ban isa ba koh?
Cike da tsiwa ta ce
“Sosai,toh kai a wa?
Kai ya jijjiga tare da hulla pillown da ya d’auka ya nufi bakin kofa.
“Yau kwa zan banbance miki tsakanin tsaki da tsakuwa..
Zumbur ta mike ganin ya dannawa kofa mukulli ya cire,ido ta waro tuno da artabunsu na ranar chan,tabbas in ta sake ya risketa tasan sai wata ba ita Deeja ba,dan haka da azama ta sakko da niyar shiga band’aki ta kulle ya riko hannunta kam.
“Yau zan nuna miki yadda zaki koyi ladabin dole ga ni mijinki na koh kin so koh kin ki..
“A mafarkinka kenan wannan, amma wallahi baka isa ba..
Shiru tai ganin ya sunkumeta sama ba tare da ta shirya ba duk da gabanta na matukar fad’uwa amma hakan bai hanata surfa tsiwa ba.
A gado ya direta tare da riketa kam yana dubenta ta inda ba yadda za ai ta kwace.
“Sosai ban isa ba,ba har yanzu da guntun bakinki ba?
Kuka ta sau mishi ganin tai duk dabara ta kasa motsi..
“Ka isa wallahi, dan Allah kai hak’uri…
Dariya ya sa tare fara abinda yai niya,ganin da gaske yake yasa ta kara jiniyar kukan nata.
“Ki adana hak’urinki,dan yau sunanki ‘Sorry’…
Cizo ta kai mishi yai saurin kauce wa,dan haka da sauri ta ce
“Mugu kawai,wallahi bana ciki da iskanci…
Kai ya dago tare da fad’in
“Ai iskanci kin barshi a baya,yanzu wannan ita ce sunnar ki mai lada in kin sa niya..
Kukan gaske tasa tare da fara roko ta Allah da annabi tana kiran Mamy.
Kamal kam yau tasan namijin duniya ne,dan tun tana da bakin roko da fitsara har cikin nutsuwa yasa tai ladab da kanta halamun ya zurmata da yawa,sai ga nan su Deeja an sau jiki ana kwasar hot messages,da sannu ya sassauta rokon da yai mata ganin ta bada gari tai surrender.
Ku biyo mu.
{SAFHA}…✍🏾
[4/4, 6:50 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION
©SAFHA
FEENAT JAFAR
SDY JEGAL
&
HAFSAT(MAMAN HANIF)
*Na gaida mutanen kirki ma’abota sada zumunci, princess Hassy, Autar Hajiya, FIdo sodangi, Sadiya Stylish, Allah yasaka da Alkairi ykr dankon zumunci AMEEN*
9
Yanayin da ya fuskanci ta shiga ne yasa wani b’angare na zuciyarsa ya soma k’aryata d’ayan sashen dake tunatar dashi k’iyayyar da Deeja ke masa.
Cikin k’warewa da son nuna mata k’warewarsa ya shiga sarrafa Deeja, wacce tunda tayi surrender ta shiga kokawa da zuciyar ta wacce ta soma k’ayatuwa da sak’onnin da Kamal yaso aika mata. Duk yanda taso ta kame kanta don gudun gori irinna Kamal amma ta kasa, a dole ta biye masa don ta kasa sarrafa kanta ji take ma tamkar ba ita bace, a yayin da Kamal ya sabunta mata duniyarta gaba d’aya.
Cikin nishad’i da matuk’ar farin ciki yake jin kansa, Kalmar hamdala ke wanzuwa cikin bakinsa tare da nanata “Ina sonki Khadeeja”. Cikin wannan yanayin mai cike da d’unbun dad’i da farin ciki ya raya darensa, wanda farin cikin ya k’ara armashine a yayin da ya samu tabbacin a iya shan mintin da suke ambata Najib ya tsaya, don haka ya k’ara d’aga darajarta ya kuma k’ara marta bata, wanda ko iya nan ya tsaya ya san baiyi zab’en tumin dare ba.
*Asuba ta gari*
Garin ya waye masa da Alkairi don wata nutsuwa yaji tana shigarsa yanajin tamkar dala da gwauran dutse ya sauke saman kansa.
Tun dawowar sa daga masallaci ya soma jiyo sautin kukanta, nan yayi turus yana kallonta, miliyoyin k’aunarta na k’ara nunkuwa cikin ransa, cikin wannan kukan bacci ya sure ta a daren jiya, gashi yanzu ma dashi ta farka, don haka ya shanye mamakinsa ya k’arasa cikin d’akin ya zauna yana saurarar kukanta wanda yai masa kama dana nadama koma kai tsaye yace na k’iyayya, duk da ya soma k’aryata wannan batun a daren jiya.
Kuka take sharb’a k’wakk’waran motsi ta kasa yi, ci kanki Kamal bai ce mata ba shi bai San dame zaiji ba, da farin ciki daya cika ransa koda rarrashin da yasan ko ya yi ba gwaninta zai mata ba? Koda murnar bata fad’a tarkonda ta shiryawa kanta ba?.
Tayi kukan ya isheta har ta sami sarari a zuciyarta, Allah ya isa kuwa babu kalar wacce batayiwa kanta ba, kuma taji kullacin tana kuka bai rarrasheta ba, bayan yasan tana buk’atar rarrashin yayi biris da ita.
Sai da ya tabbatar ta tsagaita kukanta sannan ya taso ya zauna gefenta tare da kamo hannunta ya shiga murzawa, maimakon yayi rarrashin ko yayi banbaki a’a sai ya jefeta da bak’ar magana.
“Yanzu mun zama d’aya ko? Ya juyo da fuskarta sosai suna fuskantar juna ya shiga zagaye fuskarta da yatsansa yana faman murmushi.
Bai sake tanka mata ba, kuma bai damu da sai ta bud’e idonta data rintse ba. Haka yake kalle fuskarta tare da shafa duk inda yaso a fuskarta k’aunarta na fizgar sa.
Maimakon ya fad’i kalmarda za ta sa mata nutsuwa ko su fallasa mata sirrin zuciyar sa sai ya kuma kunno ta.
“Wai me yasa ba zaki bud’e ido ki kalleni sosai ba, ko kunyata kike ji ne? ni ne fa Kamal wanda ban isaba waye ni da zaki ji kunya ko mamaki kike?.
Hakanan taji tanason kecewa da kuka don takaici da k’uncin da Kamal ya haddasa mata ga bak’ak’en maganganunsa, har wani murmushin mugunta yake mata don dai kawai ya nuna mata yaci moriyar ganga….
Don haka ta daddage k’arfin da ya rage mata ta tureshi tayi wurgi da bargon, aguje ta nufi band’akin tana gurshek’en kuka, ya bita da kallo yana dariya.
Taji dan sanyi data futo daga wankan taga d’akin a gyare hatta kayan baccinta daya dinga watsi dasu ya tsince su d’akin sai k’amshi yake.
Cikin shirin futa aiki ya shigo fuskar sa d’auke da murmushi yake duban ta harda kashe mata ido a yayin da ya matso daf da ita yakamo hannun ta ya manna mata Sumba wacce hatta yan cikin ta saida ya amsa.
Don haka ta nemi nutsuwarta ta rasa kawai sai tayi zaman d’abaro a bakin gado tana maida numfashi to baki ya mutu muruss.
cikin tattausan lafazi ya furta’ “Ina sonki, zanta sonki Khadeeja tun a daren jiya na k’udiri a niyar bautawa soyayyarki, ina so ki nutsu ki kwantar da hankalinki ki bani dama, ni nayi alk’awarin zan jagoranci cikar burin ki”.
Ya d’anyi shuru don saurarar cewarta, tayi shuru don batada abin cewa.
“Ina Neman Alfarma a gunki Deeja ki sanya mafarkina ya zama gaskiya, a daren jiya naga wani abu tare dake me kama da k’wayar sonda nake nema a gunki don Allah karki k’aryata mafarkina”.
Anan ne tasamu damar tofawa, “in dai Abinda nake ji a k’irjina na bana son zama dakai a matsayin miji ba k’iyayya bace to a gaskiya bansan kaina ba”.
Tana kai aya ya amshe, “Haka kika tab’a ganin aurenk’i? Haka kika tab’a ganin amarya bata tab’a yaji ba? Haka kika saba ganin auren k’i amarya da ango a daren farko sun raya daren salim alim tamkar wanda sukai auren soyaiya?, duk tambayarki nake yi haka kika saba gani?”.
Kunya, haushi, takaici duk ya hade mata, koma me zaice mata ita ta bada kanta daya zo da buk’ata ta biye masa har yayi galaba akanta cikin dad’in rai.
Kamar yasan abinda take rayawa a ranta, yace’ “ba kece da zuciyarki ba ba kece da gangar jikinki ba bare in nazo da buk’ata ki bijiremin, amma ko yaya so da k’i suna nuna kansu in an kasance tare”.
A zuci ta raya, yi ka gama cimun fuska kawai ka kauce”.
Siraran hawaye ne ya shiga sirnano mata bai bata damar magana ba yaci gaba.
“Ina sonki kuma zan cigaba da sonki ko yaushe, ki kwantar da hankalinki ki kori duk wata damuwa ki kwanta kiyi bacci mai dad’i a cikinsa kid’an bud’amin waje kad’an a zuciyarki da nuna so na samu na shigo, ta hakanne zamu samarwa iyayenmu farin cikin da suka zata daga garemu”.
Ya kai hannunta leb’ensa ya sunbata cikin gwaninta sannan ya saki hannun yana cewa’ “zan futa amma yinin yau aikin da na baki shine, ki lalubi zuciyarki kiji in akwai guntun sona koda jariri ne don Allah inna dawo ki sanar dani, ni nasan yanda zan raini abina ya girma”.
Wannan yad’an bata nutsuwa ta d’an rage cin magani ta kuma rage hawaye. Sai dai har wannan lokacin baiji furucinta ba.
Ya d’au tsawon lokaci yana zayyano mata bayanin da suke sata jin kunya da kuma jin ba zata yafewa zuciyarta ba, kafin yai mata sallama yabar gidan.
Nan dai ta zauna ta kimtsa kanta sannan ta futo falo, nan ma a gyare yake idon ta ya kai kan canter table wanda ke d’auke da break lafiyayye daya shirya mata, don haka bata tsaya b’ata lokaci ba ta hau ci don wata mahaukaciyar yunwa take ji, taji dad’in roman naman kajin da yayi mata wanda yaji kayan had’i tas ta shanye roman ta bar ragowar naman.
Komawa tai d’aki ta kwanta bayan ta gama break d’in don duk bata jin dad’in jikinta, duk jikinta yayi sanyi ta sawa ranta Kamal ya riga ya gama cutarta dole inya dawo ayita ta k’are.
Cikin wannan zullumin ta yini.
A nasa b’angaren kuwa? Yini yayi cikin nishad’i da begen matarsa don ta shayar dashi mamaki don haka yini yayi yana tunaninta, gangar jikinsa ce a gurin aiki amma hankalinsa na gida, har a gurin aikin abokansa sai da suka fahimci farin cikin da yake ciki, don shi kad’ai yake zuba murmushi a duk sanda ya tuna daren Alfaharinsa.
Karfe hud’u na yamma ya had’o yanasa yanasa yadawo gida don ya kasa aikin kirki.
Ku biyo mu
SAFHA….✍🏻✍🏻
[4/4, 6:50 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION
©SAFHA
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
MAMAN HANIF
10,
*godiya ta musamman gareku masoyan Ina da buri*
Cikin nishad’i yashigo gidan harda wak’ar gwanin sa Maher Zain a bakin sa yana rerawa hannun sa rik’e da lodoji guda biyu cike suke da kayan kwalam wanda yasan tanaso don ita inhar da kayan kwad’ayi to abinci ma bai dame ta,
Turus yaja ya tsaya don tsantsar mamakin ganin a yanayin daya barta haka yadawo ya sameta, gefe guda Kuma ga akwatina nan guda biyu cike da kaya,
Saida yakare mata kallo tsaf yagama karantar rikicin data tanadar masa duk batasan yana tsaye yana kallon taba sai cika take tana batsewa ta had’a gumi sharkar idon ta face- face da hawaye, don haka ya dauke wuta ya murtuke fuska don yaga inbaiyi da gaskeba Deeja k’arfin sa zata fi.
Tun dazu take jiran dawowar sa da taji motsin dirar mota zata fara hade fuska tana yatsina tareda kirkiro rashin mutuncin da zata shuka masa harta gaji da jiran sa takoma d’aki ta kwanta bayan tagama fakin din kayan ta don tagama sawa ranta tagama kwana a gidan kamal
Batai auneba saijin muryar mutum tayi akan yana magana fuska a had’e da cewa”
Don Allah taimaka kid’an dauki hutun kukan nan kona minti goma ne ki duba kayan nan dana shigo dashi ciki akwai gasasun kifi ki zubomin naci yunwa nakeji, inna ci na kauce Alla bashshi saiki d’ora daga inda kika tsaya”,
A fusace ta taso masa” inna bar kukan sarari na zuci nake don nida hutawa da kuka ina zatan sai ranar da k’asa ta rufe ido na”
Cikin ko inkula yace” babu laifi had’iye kukan da dukkan damuwar taki kije ki zubomin bai kamata ace nikuma taki damuwar ce zata kashe Niba….. ta ina kukan ki ya shafeni da zan nemi abinda zanci na rasa?
A k’ufule tace” kaga malam niduk ba wannan ba jiran ka nake dama kadawo daga Yau nagama zama dakai don wallahi nagaji bazan iya cigaba da rayuwa da mak’iyi naba, Allah wadaran auren had’i da Wanda bai iya soba baisan soba kuma bai iya tarairaya ba saidai yasa k’arfi, to bari kaji a shirye nake dana karbi saki a hannun ka kuma Allah ya isa iddar da ka d’ora min”
Cikin salon shanye mamaki ya zaro ido? ” idda? Wacce idda kuma daga gwaji? Ai tukunnama yarinya wancen na jiyan ae sharar fage ne don haka karki damu kanki, so kuma ai gajen hakuri kikai bakiga komai ba ”
“Mtssw ” tasaki tsaki, ” Allah ya kiyaye Kamal kayi kad’an ka siffanta kanka cikin wanda zanyiwa kallo irinna so kaikan ka kayi ganganci don kasan ban tab’a sonka ba kuma bazan tab’a son kaba, kullum addua nake Allah ya nunan ranar da zan wayi gari a gidan ubana ba a cikin wannan kurkukun ba”
Cikin yanayin tura haushi yace” dad’in abun dai babu Wanda aka kafe da k’usa a cikin gidan”
Zuwa yanzu kukan ta yakaru, ” Na shiga uku nidai Allah ya hadani da jangwam narasa wa zanyiwa Allah isa da aka dulmiyar min da rayuwa ta aka rushen buri na”!
” au da kinada aikin neman Wanda zakiwa Allah ya isa kika zauna aikin dabazai fishshe kiba?
“Kasake ni Dan girman Allah nakama gaba na kamal kowa yayi abinda zai fishshe shi,”
“Kanki akeji”,” wlh da ace igiyar kadararran auren nan a hannuna take da tuni nai maka saki d’ari ma inda anayi”
“To dama wazai bawa mahaukaciya rikon igiyar aure?aike da igiya saidai igiyar gugan da Zaki ja ruwa inna gaji da tab’ararki na maida ke k’auye”
Bak’in ciki ya kulle ta takasa magana, can dai ta Dora gannu aka ta kurma uban ihu” wayyo mamy!!!
“Allah ya tsinewa wanda ya aminta dani matar sace Allah ya isa ban yafe ba”
Cikin d’aurewar fuska ya daka mata wata razananiyar tsawa wacce bata ta’ba zatan ya iya taba, ” yimin shuru!! wawiya kawai wacce batasan ciwon kanta ba, ki tsaya kinutsu kisan mecece rayuwa don wannan kwanyar kan naki ni bansan menene a cikin sa, inataya Abba jimamin asarar kud’in tarar da yayi akanki don wacce tafuto daga turu ma tunaninta yafi naki tsafta”
“Kuma wannan kashedin da zanmiki yazamo Na farko kuma na k’arshe inna kumajin bakin ki yafurta Kalmar saki ko Allah ya isa saina zubar miki da hak’ora”
Duk da tad’an tsorata da ganin b’acin ransa amma saita maze don batada tsoro.
Cike da tsiwa ta turo baki takama murgud’e shi tana fad’in” babu Wanda ya isa ya fasamjn baki in kuma mutum yasake ya tab’ani ya daki auren sa, aikin banza aikin wof….ae bata k’arashe ba yasa hannu ya gwab’e mata bakin, take tasaki k’ara harda buga tsalle ta dire tana rik’e da bakin”
Wallah bazan yarda ba Saina rama aiki babu abinda mutum ya iya saicin zali da mugunta abin yayi tsamari harda duka toni a gidan mu ban saba ganin duka ba”
Ya tari numfashin ta” Nina saba kuma in kin isa kifad’i abinda abinda na hanaki fad’a”
Nan takasa magana takama k’unk’uni tayi hanyar band’aki tana kunkuni,” oho dai nafad’a kuma nak’ara kuma wallahi bazan yarda ba saina rama mugu azzalimi”
Baijita ba sosai don tayi nisa dashi,” naam me kikace? Cikin murgud’a baki tace” saina rama”, ” zoki rama nisainazo ma har inda kike ki rama d’in”
“Ban yafe ba wlh har duniya ta nad’e, aikan yayi wani Abu ta afka ban’dakin ta murza key, ganin yayo kanta a fusace,
Gaban tane ya dinga fad’uwa don tasan jiran ta yake tafuto ba kyaleta yayi ba ga magriba takawo kai ga duhu yan NEPA sun dauke wuta.
Duk tsoro yacika ranta jin shuru babu motsin mutun yasa tayo alwala ta futo don tuni masallaci sun idar da sallah,
Cikin sand’a tafuto tana waige waige batai aune ba sai jitai an damko ta ta baya, nanfa ta kwalla ihu yayi saurin toshe bakin ta,
” meye na tsorata dawowa nayi kirama fa” cikin in ina tasoma” uhm un mefa? Ni aina hak’ura tun d’azu kuma ae ba canai zan rama ba”,
Rik’eta yayi sosai tana k’ok’arin kwacewa”ni ae yanzu nace kirama ko? Baki yarda da Abinda nace miki bako? Shine kika kuma yimin Allah ya isa”,
“Aa nifa ba Allah ya isa nayi ba canai ban yafe ba toma kayi hakuri Dan Allah sakeni nayi sallah tukun wallahi sub’ul da baka nayi, takama dukan bakin ta,
“Oh ni bansan me yake damun wannan bakin ba inaga ungozoma bata gasashi yanda Yakama taba”
“Tom shikenan yi sallar saina gasa miki”
Yana sakin ta batayi wata- wata ba takama sallah, yana tsaye ta idar, yayi zatan tana shafawa mik’ewa zatai aa saita kuma tayar da wata,
“Aa ikon Allah” yafad’a don ganin tanata jero sallah tun yana lissafawa harya b’ace a raka’a ta kusan goma sha biyu ya dakatar da ita da cewa”ke Dakata!!!
Kubiyo mu.
SAFHA
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
SDY JEGAL
FEENAT JAFAR
&
HAFSA(MMN HANEEP)
11_Sallamar da sallar tai tare da juyo wa.
“Ya isheki haka..
Ido ta zaro..
“Wa ya fad’a ma sallah na isa? Koh ka manta Nana Aisha cewa tai annabi har kumbura kafafunshi suke dan ibada?
Harara ya sau mata,
“Ji ta agun,kamar wata ta Allah..
Rai ta had’e.
”Mey ka ke nufi?
Banza yai mata tare da komawa ya kwanta ita kuma ta cigaba da jero sallah.
Ganin abin ba na hankali bane yasa ya raja’a a baccinshi.
Juyo wa tai tare da tashi cikin sand’a ta leka shi,ai ta gano take taken shi,anshata jiya,dan haka *Dan ba kara wai haihuwar shege*.
****
Duk yadda yaso ya samu kusanci da ita abin yaci tura,ya yi na Allah,ya yi ba annabi,ya sauke duk wani girmanshi gaban Deeja amma bai jin ya ta6a cin karo da mai taurin kan Deeja,gar da gar take nuna bai isa komai ba,dan haka ba karamin jin haushin kanshi yai ba da har ya iya tona mata sirrin zuciyarshi amma taki amsa.
A ganinshi ya bada kanshi gareta da har ya zamo soko.
Dan haka da bak’inshi ya hau warware cewar shi fa da wasa yake,ta ma daina wani rawar kai.
“Dan fa you’re are not my type..
Baki ta ta6e tare da daga kafad’a
“Daga baya kenan wai anyi sadaka da karuwa,dan soyayyar ka sani kad’ai a baki,amma baka iya ta a aika ce ba..
Murmushi ya yi tare da jijjiga kai kawai ya cigaba da abinda yake,ya sani da tai nisa,nisan da bazata ji kira ba,a ganinshi ta hanya d’aya zasu dai daita da Deeja,dan haka yasa kafar wando d’aya da ita.
Daga ranar ya fara seta kanshi da Deeja,bai sake sakacin sanarta yana sonta ba balle yasa dole ta sau ra’ayinta.
Dan haka yanzu aka dawo takun saka a tsakanin su.
***
Yau gida ya shirya ya ce suje gaisuwa tun bayan tariyarsu.
Sosai tasha fad’a da nasiha gun Mamy da Abba duk zancen d’aya ne,tabi mijinta sau da k’afa, dan haka a cike dam suka dawo gida duk yana hankalce da ita.
Baki a d’ane ta dubenshi ganin ya sakace d’akin tare da zuba mata ido.
“Lafiya kuwa? Kamar wanda ka ke bina bashi irin wannan kallon?
Kai jijjiga tare da murmushin mugunta.
“Bashi kuwa turum,yau kuma zaki sauke shi.
Yawu ta had’iye da sauri ganin ya fara kunce buttons na rigarshi yana murmushin mugunta in yaso mata keta yana karasowa,dan haka tuni ta fara raba ido da tunanin abinyi.
Hanci tai saurin toshe wa tare da k’ak’alo aman karya tana daga mishi hannu.
“Kar ka karaso, amai nake ji..
Tsaye yai tare da sa mata ido,da gudu tai hanyar band’aki tana k’ak’arin aman karya ta barshi baki sake.
Chan dai ta fito tana yatsine fuska,
“Zuciyata ke tashi in kana kusanto ni kamar nai amai..
Galala yake dubanta kamin daga
“Mey ki ke nufi kenan?
Zama tai a bakin gado tana dan cije le6e..
“Wash Allah cikina,anya kuwa ba ciki gareni ba?
Ido ya zuba mata baki sake ganin zata raina mishi hankali.
“A sati biyu dama ciki yake baiyana ‘yar fama?
Rai ta had’e tare da kalloshi..
“Toh mey ka ke nufi? Karyar ciki zan maka komai? Kasan dai zanfi kowa bak’in cikin ace ina da ciki da kai..
Tsam yai yana tunani,so yake ya gaskanta amma ya kasa,sannan ya kasa karyata ta.
Baki ya ta6e,
“Allah raba lafiya,amma ba shi zai hana ki sauke bashin da ki ka d’auka ba..
Zirif ta mike tare da d’ane wa kan gadon ganin dabararta batai ba.
“Wane irin mugu ne wai kai? Na ce ma ban son ka rika kusanto ni zanyi amai..
Gadon ya d’ane tare da janyo hannunta ta fad’o kusa dashi.
“Karya ki ke yi,kuma wallahi sai kin amsa..
Kokawa suka fara sosai,amma dake ya gama gano lagonta da sannu ta bada kai bori ya hau,komai na lafawa ta hau kukan ya cuceta yai mata keta.
Harara ya sau mata lokacin da ya fito a bayan gida har lokacin tana kuka.
“Ki ma ware yarinya ki amsa da lada in kin sanya niya,ni bana ciki da kinibibin karya.
Jiniyar kukan ta kara yana tayata, dan haka sai ta hau hullo mishi pillow yana mata dariyar keta.
Washegari weekend ta kama,ba kero ba gas,dan haka dole ya d’au flaks dan koh motsi taki yi ta tafi gun mai shayin kwanar gidan da jarka a hannu.
Mai barkwanci ne sosai mai shayin, saurayi ne,amma tuzuru,auren ne bai da wuri ba.
Sosai sukai sabo dan a gunshi yake siyan biredi.
Dariyar keta yai ta mishi wai mey zai da flaks? Hala dan kuturin ya motsa?
Kai ya jijjiga yana murmushi
“Za fa kai auren nan ne,za ka gane komai yanzu koh na fad’a ma ba gane wa za kai ba.
Kai ya jijjiga yana zuba mai tea,har da su kwai ya dawo,Allah ya bashi Deeja sai dai ya gode.
Karfi da yaji ta tsiri mishi laulayin karya kawai dan ta wahalarshi.
Haka zai shiga kitchen ya zage yai mata girki wai wari kitchen din yake,haka zai dafo ya kawo mata.
Sai ya kauce tai ta dariyar keta.
Bawan Allah tun baya yarda har ya yarda da gaske ciki gareta,sai dai iskancin Deejan ya fara over.
Karfe takwas na dare yana zaune ta fito a d’aki tana yatsina fuska.
Da harara ya sau mata tare da d’auke kai yana sauya tasha.
Baki ta turo tare da ja ta tsaya a gefe.
“Ni fa d’an wake nake son ci,shi nake marmari..yanzu.
Kai ya dago tare da zuba mata ido,a gaskiya Deeja bakar muguwa ce,yanzu ya gama wanke-wanke bayan yai mata girki taci ta hantse.
Dan haka cike da hatsala ya ce
“Koh kinfi uwa yata mayya yau baki isa na sake shiga kitchen ba Wallahi kinji na rantse…
Juyo wa tai tare da had’e rai,
“Ba sai ka rantse ba,dan nima d’an cikin nawa d’an waken waje yake so na siyar wa ba naka ba,in ba zaka siyo ba sai na fita da kaina..
Jim yai yana k’are mata kallo,ganin yaki tashi yasa ta sau kukan karya tana buga k’afa,kwafa ya yi tare da tashi ya shiga kitchen ya d’akko flaks.
Harara ya dalla mata tare da d’aukan torchlight ya fita yana jijjiga kai,lalle dole ya d’au mataki dan gano shin cikin gaske ne koh kuwa karya?.
Dariya take harda rike ciki bayan ya fuce,harda y’ar kwallar mugunta.
Gabar ya kalla ya kalli yamma,ya ma rasa ina zai dosa?
Mai shayi ne ya fad’o mishi,dan haka kawai sai ya kad’a kai tare da nufar wajen.
SAFHA…✍🏾
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
12_Ko da ya iso gurin a cike ya tarar da shi da mutane ‘yan zuwa domin fira wasu dan cika kundunsu da shayi,yayinda wasu ke musu akan ball.
Guri ya samu ya zauna yana saurarensu,har ya tuno lokacin yana single ba wata matsalar cikin gida kamar su mai shayi.
Ganin sun d’an ragu ne ya sa ya tambayi mai shayin inda zai je ya siyo d’anwake a yanzu.
Duk ido suka sa mishi da mamaki,
“Kai zaka ci?
Kai ya girgiza tare da fad’in
“Mai d’aki na ce..
Dariya sosai su ka harda kyakyatawa.
“Shi yasa nake jin dad’in gauranci watarana, in banda haka a wannan tsohon daren a ina zaka samo d’an wake?
Dariya suka sake sanya wa,dan haka tuni ya sake kuluwa iya wuya.
“Hadi,mu munyi nan,dan an kwaso maka aiki..
Hadi dake tattare kaya ya jijjiga kai,
“Yanzu Hadi ace kai ne a matsayin da nake a yanzu mey za kai wa matar ka?
Baki Hadi ya washe yaji anzo gurin,
“Jirani kai dai na gama had’a kayan nan.
Kai ya kad’a.
Nan ya had’a duk wani abin buk’atarshi sannan ya cewa Kamal ya biyoshi.
Yanda kasan rak’umi da akala hakan Kamal ya bishi har suka kai shagonshi.
Bayan ya sauke kayan sannan ya yiwa Kamal nuni da cewa ya zauna,ba musu ya zauna.
“Wato in ne a matsayinka abokina ka ga nan?..
Katifa ya nuna mishi da hannu,dan haka sai ya gyad’a kai.
“Zuwa zanyi na kwanta a nan,in safiya tai
“Kawai shawara guda zan baka,kayi kwanciyarka anan,in yaso da safe sai na raka ka inda ake siya ka siyo mata,in ta tambayi dalili ka ce mata da kaje layi ka samu a cike,shine kabi sahu sai yanzu yazo k’anka…
Tsam ya yi yana tunanin dabara irinta Hadi wacce shi bai ma yi tunaninta ba,yasan in yai haka toh ba makawa ya toshe wannan bangaren,dan haka ba musu ya yarda.
“Kai Hadi na gode,lalle kasan takan mata.
Dariya ya yi sosai sannan yace
“Yo,ai ba banza naki aure da wuri ba,so nake nai degree a karatun dabiar mata da matsalolin su,ka ga yanzu ma na samo solution na had’i da wata formulan.
Da sauri ya ce
“Allah Hadi?
Pillow ya gyara tare da niyar kwanciya.
“Sosai kuwa,waya gaya maka cewa duk abinda Mata ke so ake yi masu? Ai inn ka biye musu da hakan zaka wahala wallahi, don ina mai tabbatar ma watarana har d’anwaken za tace ba zata iya taunawa ba sai ka tauna ka bata ta had’iye”…
Dariya suka sa harda tafawa,shi dai burinshi wacce ya yi dominta taji jiki,gaba ta gane akwai banbanci.
Hakan kawai yaji shawarar mai shayi ta kwanta mashi a rai, nan ya biye mai suka yi kwanciyarsu.
****
6angaren Deeja kuwa tana ganin cewa har k’arfe 11:00am ba Kamal ba labarinshi hankalinta gaba d’aya ya soma tashi,sai sintiri take yi daga falo zuwa d’an tsakar gidan.
Bata k’ara tsurewa ba sai da taga agogo ya nuna k’arfe 12:00am, nan ta janyo wayarta ta kira wayar Kamal wacce ranar ya kira ta da ita hankalinta a tashe.
K’arar wayar data jiyo d’aki ne ya yi dai-dai da sakin wani nadamammen kuka nata, yi take yi babu k’akk’autawa, duk inda hankalinta yake a tashe yake, ji take yi tamkar ta fita nemanshi.
Tayi da na sanin wannan karyar cikin gashi ta jawo Kamal ya 6ace.
Kukan da take yi,iyakar iyarta,chan ‘yan gida suka fad’o mata,dan haka da sauri ta hau kira.
Kashe wa tai da sauri dan tuno da mey zata ce toh in an tambayeta?
A tsohon dare ta sashi fitar dole ya siyo d’an wake koh mey?
Kuka sosai take,bazata iya ba,tuni kanta ya fara sara mata, sai dai ita ba wannan ce damuwarta ba, damuwarta d’aya taga ta ina Kamal zai 6ullomata, nashe-nashe kawai take yi a ranta inda abin ya fi tsaya mata a Kamal ya rasu, nan ta sake tsallara kuka tamkar zata tsage mak’oshinta.
Ranar bacci sai 6arawo,bata san lokacinda ya yi awon gaba da ita ba. Kiran sallah ne ya tayarda ita sai wani jiri take gani kanta na mugun sara mata.
Dube ta fara ganin a parlour ma tai kwanan zulumi.
Hawaye ne ya zubo mata ganin kofar a garkame halamun bai shigo ba.
Hannu ta aza bisa kai tare da furta
“Wayyo ni Deeja.
Sai ta sake dasa sabon kuka,ranar har period d’in dole ne yazo da asubar.
Gari nayin sha ta fito dube Kamal kam wayam har karfe takwas.
Gida ta koma tana ta kwata kiran gida amma ta kasa da sauri tana ta katse kiran.
In ka ganta abin tausayi idon nan yai luhu-luhu.
Shin wannan din nadama ce Deeja? Koh kuwa Kauna ce?
SAFHA….✍🏾
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
13_A zube take bisa kan tiles tayi d’ai d’aya cikin kukanta tamkar an aiko mata Mamy ta mutu,sai kunji kuka take.
Cike da sand’a ya turo kofar yana mai cije hak’ora kamar mai tsoron kar taji.
Galala ya yai ganin yana yin da take ciki,tuni ya fara kunshe dariya ta juyo.
Kukan ta bari tare da zuba mishi ido,kan yai magana har ta zabura tai yo kanshi da gudu ta ruk’unk’umo shi tana kuka.
Dariyar ya bari tare da sauya fuska cike da mamaki,tunaninshi shin mey hakan yake nufi?
Ba dai Deeja ta damu da rashin dawowarshi bane?
Dago kanta yai idonta rintse tana shesshekar kuka da fad’in
“Wallahi na zata wani abu ne ya faru,tunani na koh ka mutu ne…
Rai yai saurin had’e wa jin zancenta tare da maka mata harara.
“Muguwa kawai,in na mutu ai nasan bakki asara.
Ran itama ta had’e tare da kwace jikinta ta hau nad’e taburmar kunya.
“Da wa ya damu da ka mutu koh kai rai? Ka san dai ba damuwata bace,dan tabbas bani da asara.
Kai ya jijjiga tare da ajiye flaks din d’an waken,yasan koh ba komai ai taji jiki.
Wuce wa yai hanyar d’aki yana kunshe dariya,kan ya zata tasha gabanshi.
“Sai ka fad’a min inda ka kwana?
Rai ya had’e tare da dubenta.
“Ina ki ka aike ni?
K’ugu ta rike tare da fad’in
“Kana nufin tun jiya d’an wake ka ke nema?
Kai ya jijjiga da sauri tare da fad’in
“Shine amsar,dan cike na samu layi a gidan,kinga dole nabi sahu sai yau yazo kaina…
Kallon kar ka rainan wayo tai mishi.
“Gidan wace matar ne za’a je a samu d’an wake a wannan daren balle har a samu layi har yau?..
Kai ya ka’rkar da sauri tare da fad’in
“Oooo,ashe kin san ba a inda zan samo d’an wake cikin tsohon daren amma ki ka fidda ni?
Baki ta chunno tare da d’auke kai jin ta kwafsa.
Kai ya jijjiga tare da fad’in
“Good,dan kiyi wa kanki..
D’aki ya shiga ya batta sai masifa take na fad’in toh mey ya cinyeta? Mugu ai dama yasan mey ya had’a, kuma baza’a ci dan waken ba.
Kofa ya turo yana daga mata kafad’a, yasan yai mata d’aya, ba ta inda zata huce takaici,dan haka dariya ya rika dirka kan daga bisani ya bi lafiyar gado dan yasha shayi gun Hadi.
Bayan yaci abinci rana yai wanka ya fuce dan har lokacin da harara kawai take binshi da kwafa,yasan ba yadda zatai dashi sai hak’uri.
Maman Ihsan ce ta shigo jin ya fita da mota.
Cike da tuhuma take kallonta dan har kukanta na duben Kamal tana jiyo wa a tsakar gida.
Koh da ta tambayi ba’asi ba abinda ta 6oye mata.
Kai ta jijjiga,
“Mugun dad’i ne yai miki yawa,amma ki sani kina wasa ne da damarki,zan so kiyi amfani da ita tun kamin ta ku6uce miki,dan miji ba abokin hamayya bane,gashi a karshe ke ya bari da kukan da na sani..
Da sauri ta girgiza mata kai halamun a’a ne.
“Ni ba shi nake wa kuka ba,tsoron duk girman gidan nan yadda ni kad’ai aciki ne kawai ya sani kuka,amma dan tani ya mutu ma man shi ta shafa bani ba…
Murmushi Maman Ihsan din tayi tare da jijjiga kai,bata jin ta ta6a cin karo da mai shegen taurin kan Deeja,amma ta sani Kamal ne kad’ai maganinta,abu d’aya take guje mata yadda take wasa da damarta, dan in auren soyayya ne taga kawarta da mijinta, dan soyayya a titi har ‘love birds’ ace ce musu.
Kai ta jijjiga.
A rayuwa ta sani Deeja abinda ke gaba gareta kawai take duba,amma Insha-Allah wataran zata kai ta gidan k’awarta,tasan daga ranar Deeja sai ta sauke Buri da rayuwar soyayya zallah a gidan Miji..
Murmushi tai mata,dan a zahiri koh ita bata yarda cewar Deeja na da ciki ba,dan a d’an zamansu ta fara karantar halinta da tsabar kafiyar ta.
Zancen tace a bari,dan wai koh sunan Kamal taji yana sa ta kara jin haushin shi.
Sallama tai mata lokacin karfe biyar da wani abu ganin Kamal din ya shigo.
Koma wa yai bayan ya d’akko mata hijab tare da fad’in da bako suke, sai murmushi yake yana jijjiga kai,da kallo ta bishi,tabbas da abinda yake neman had’a mata.
Nurse ne rike da yar akwati dasu abin auna ‘Bp’.
“Bissmillah karaso ciki.
Tsaye ta mike tare da fara raba ido had’i da tattaro yawun bakinta ji ka ke kwat! Ta had’iye.
Kallota ya yi,a duniya yasan ba abinda ta tsana sama da allura,yasan ta hakan ne kawai zai gane gaskiyar lamari.
“Sannu madam..
Ido a ware take kallon Kamal din gabanta na fad’uwa ta kasa koh amsa sannun Nurse.
“Gata nan dai Ishak,ka ganta nan tun samun cikinta laulayi ta kasa sukuni,yau zazzabi gobe ciwan kai,gashi in ta fara k’ak’arin amai har tausayinta nake ji…
Wani yawun ta sake had’iye wa tana goge zufa tare da sake waro ido.
Lalle ne in baka iya kama barawo ba shi sai ya kamo ka..
Tsayuwa ta gyara ganin yana fito da ruwa na karin ruwa da allurai,da sauri ta fara in ina.
“Malam ni fa lafiya ta kalau wallahi, ba wani zazzabin da nake da amai..
Da sauri Kamal din ya amshe da fad’in
“Rabu da ita Ishak haka take in taga allura,amma mace mai lalurar ciki ai sai da protection,har da ta tetanus ma kai mata..
Lalle kam Kamal ya wuce tunaninta,dan haka gaba dole ta iya bakinta da tukunta,gashi yanzu yai mata back to sender,dan haka da azama ta karyata kanta da kanta.
“Wallahi ni k’arya nake,ni bani da wani ciki,dan haka ba allurar da za’a min da raina da kuma lafiyata..tab,humm.
Kai ta juyar tare da matsawa gefe tana aiko mishi da harara,shi kam bai mamaki ba,dama bai sa a ka ba,amma dan ya taka mata birki yake son sanin gaskiyar lamari,gashi tun kan ai nisa ta karyata kanta,dan haka da sauri ya ce
“Karya take,dan haka baki isa a fita daga gidan nan ba tare da an juna miki ruwa da allurai ba,dan kin san na sani da kullum sai kinyi amai kusan sau goma,koh so ki ke ki yanke jiki ki fad’i ruwan jikin ki ya kare?..
Murmushi Nurse din yai tare da kad’a kai,ya sani da mata akwai tsoron allura,dan haka sai ya ce
“Kiyi hak’uri madam ayi a nutse mu gama,guda uku ce kawai sai ruwa hud’u..
Ido ta zaro tare da bud’e baki,kamin ya sake magana har ta sau kuka,fad’i take ita sam karya take,lafiyarta lau dan haka ba mai kasheta da ranta.
Kanta Kamal din ya nufa batai tsammani ba ya chafko hannunta,
“Ai kinyi kad’an, naki wasa ne,dan fa ba kuka ba koh suma ki ke sai an miki..
“Wayyo Mamy na shiga uku.. Wallahi karya nake maka ka rufa min asiri Kamal,bazan sake ba kaji na rantse..
Kai ya girgiza mata yana mai kunshe dariyarshi dan kar ta gane,a take yai rantsuwa da sai fa an mata,zo ka ga Deeja gwiwa bibbiyu gaban Kamal tana rokon yai mata rai ganin Nurse na zoko ruwan allura.
SAFHA..✍🏾
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
© SAFHA
SADY JEGAL
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSAT ISMAIL (MMN HANEEF)
_Yan Uwa muna barar addu’arku zuwa ga yaronmu Muneeb, Allah ya bashi lafiya ya d’auke lalura, da sauran dukan musulmai baki d’aya_.
14_A tsaye yake hannu bisa ha6a yana dubenta fuska d’auke da murmushi lokacin da take kunjin kukan ruwan da tana ji tana gani ya matseta aka mamuka mata.
Kuka take harda shessheka,ta yarda Kamal ya wuce tunaninta,dan a fagen mugunta tasan in za ai competition toh ba abinda zai hana yazo 1st position.
Yau tun tana da karfi amma sai da ya nuna mata karfi gun amsar allurar karfi da yaji,Allah ya isa ta fad’eta tafi dubu acikin ranta,dan yanzu har tsoron fidda tsiwarta take a fili, dan tasan sai ya fanshe.
Tana nan har baccin dole ya sureta,in banda ‘yar harara ba abinda take aika mishi sai kuwa kuka,maganin karya kam,wai hallara.
Ido ta bud’e a hankali jin ‘yar hayaniya a kanta,Mamy ce da shi su na dubenta.
Baki ta fara ta6e wa halamun kuka ganin Mamyn.
Karaso wa yai hadda fad’in
“Sannu,kin tashi?
Kuka ta saka,dan haka sai Mamyn ta matso shi kuma ya hau k’ok’arin cire mata ruwan ya fuce.
Da dan tausayi Mamyn ta bita da kallo wanda ke nuna alamar duk ta fara zabgewa, nan kuwa Mamy bata san cewa zabgewar masifa bace da rashin kwanciyar hankali.
Sannu ta yi mata had’e da jefo mata tambayar lokacin Kamal ya dawo rike da kofin ruwa akan faranti
“Koh dai laulayi ne ke damunki?…
Shiru tai,duk da Kamal din yaji zancen amma sai ya kalleta,da sauri ta girgiza wa Mamyn kai
“A’a ba shi bane..
Dariya Kamal din ya kunshe,a ranshi yana fad’in
”Wuya kenan..
Kai Mamyn ta jijjiga,
“Amma ance harda amai fa Deeja…
“Allah Mamy banda komai ciwo ne kawai, kuma ma naji sauk’i”.
Kai Mamyn ta kad’a.
“Toh Allah ya kara afuwa.
Baki washe Kamal din ya ce
“Amin Mamy, ga ruwa.
Ido Deejan ta kulle,koh kad’an bata son kallonshi tunda bazata iya gasa mishi magana ba.
Bayan Mamy ta d’an yi mata nasihar kula da kanta ta tashi Kamal ya rakata ta tafi, sannan ya dawo d’akin yana mai k’unshe dariyar mugunta.
Ido ta bud’e tare da kafeshi dasu.
“Wai mey ka ke nufi dani ne?
Zama ya yi tare da gyara mata filo.
“Abinda ki ke nufi dani My Deejalo..
Hannu ya kai gefen kumatunta zai ja tai saurin make hannun.
“Bazan ta6a yafe wa ba tunda ka zalunce ni, macuci kawai azzalumi mara tausayi, ai nasan fiye da hakan ma zaka aikata a kaina,mara tausayi, wallahi sai Allah ya saka min”..
Kuka ta saka,dan haka da sauri ya sha mur.
“Wato har yanzu kina da bakin tsiwa koh?
Banza tai mishi,cuta kam ya riga da ya cuceta,bakin cikinta d’aya kar wata cutar ta sameta tunda lafiyarta kalau.
Tun daga wannan ranar ta fara kama kanta,zai wuya ta tanka mishi sai dai harara daga nesa,dan ba karamin tsorata tai da sharrin Kamal ba da yafi na mata d’anuwa,ta nan kam ya samu sa’ida.
***
A gaban mirror take tana shafa mai had’i da dan harararshi,yayinda shi yake zaune kan gado sai murmushi yake yana shafa ha6a,yau kusan sati biyu tana mishi karyar period take,gashi yau ya kamata tana ruku’u.
“Wato baki daddara da karya ba koh?
Kalloshi tai tare da shan mur.
Shiru tai tare da cigaba da abinda take,dan ba karamin sanyi ake ba ga ta debo wankan da ya zame mata tamkar dole na dare.
Sakko wa yai,shi har ya yi missing tsiwar nan ta kwana biyu da ake mishi yanzu sai harara daga nesa.
Man ya dangwalo yana yana shima yana dan hararar tata.
“Ki sani lissafi za ai,dan wannan sati biyu sai kin ramata a yau…
Baki ta bud’e ganin wani karfin hali ganin ya riko hannunta yana shafa mata mai.
Zumbur ta mike tare da k’ank’ance ido zata fara bala’i ta tuno da karan baya dan haka sai ta matsa tare da fad’in
“Bana so,ka fita kuma harkata…
Tashi yai tare da janyota da d’an karfi ta taho gareshi.
“Karya ne wannan, dan haka kar ma ki wahalar da kanki.
Tureshi tai da sauri tare da matsawa ganin yana neman samo lagonta.
“Wai in ba kai mugunta ba baka jin dad’i ne?
Kai ya daga da sauri yana mai matso wa.
“Ai gunki na koya,koh kin manta?
Baya ta fara ja tana had’iyar yawu.
“Naji, duk da haka wallahi kar ka ta6ani..
Chafka ya kawo mata da sauri ta zille gefe.
Kai ta jijjiga,
“Wato so ki ke mu zama kullum Tom and Jerry koh? Wanda basa jituwa sai sunji jiki koh?
Kai ta kad’a da sauri
“Ai bazan ta6a jituwa da kai ba kasan wannan..
Tsalle ya doka tare da ritsata lungu.
“Nafi son haka,dan yana kara sa minke ladabin dole..
Magana zatai,sai dai kan ta kai ga furtawa ya chafkota,kamar kullum dai yau ma shi yaci nasarar sata lagwas,sanda komai ya lafa kamin ta hau kukan ya cuceta.
SAFHA…✍🏾
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
15_Harara ya sau mata tare da fad’in
“Saura carry over..
Baki ta saka,kan tai magana ya chafki bakin dan sa mishi sakata,wuya kam tasha ta yau,sanda ta rika rokon ta daina karya dan Allah yai hak’uri tukunna ya kyaleta yana gyad’a kai na mugunta.
Gaskiya ta fara tsoron Kamal,ketakar shi mugun yawa gareta in har ya furta,dan haka tuni ta ajiye makamenta tai surrender, dan komai zata mishi,toh Insha-Allah kanta abin zai kare,dan ita ke jigata.
****
Zaune take bisa gado ta tankwashe kafarta tana dubenshi,da ya kallota sai ta dauke kai tare da ta6e baki.
Link yake sawa na riganshi gaban mirror yana dan mata murmushi, sosai yai kyau cikin fararen kayan halamun zashi sallar juma’a ne.
“Ki fito ki ce ‘Habeebi kai kyau’ kawai ba ki tsaya satar kallona ba..
Sama da kasa ta kalleshi kamar taga kashi tare da ta6e baki.
“Allah sauka min,dan ni dai banga kyau anan ba sam..
Murmushi yai tare da gyad’a kai tare da sanya hula ya tako gaban gadon tare da d’aukan sallaya.
“Kyaji da shi dai,wai gad’a a makabarta,ni na wuce,zamu dawo tare da su Salis.
Baki ta ta6e tare da shirin magana ya dan mako bakin yana harararta.
Da hararar ta bishi har ya fuce hannu bisa baki,a hankali ta ce
“Mugu kawai…
Kai ya leko dashi tare da fad’in
“Mey ki ka ce?
Ido ta waro, ba dai wai yaji ba?
Da sauri ta girgiza kai tare da fad’in
“A dawo lafiya na ce..
Murmushi ya yi tare da kanne mata ido d’aya
“Sai na dawo.
Yake tai mishi, dan haka sai ya tafi yana jijjiga kai,tabbas Deeja tai laushi wajen tsiwa,abu d’aya ne taki ta sauke,ta kuma ki ta kalleshi a matsayin masoyi sai babban makiyinta.
*****
“Ni dai ina rabaki da wannan dabi’ar ta kafiya wallahi, ace ni na samu kamar mijinki k’awata wallahi babu mai jin kanmu..
Baki ta ta6e tare da gyara zama.
“Kin san Allah Kamal bai d’ad’ani da kasa ba,cuta ce an riga da an cuce ni,duk wata dabara da zai sauwake min nayi amma ban samu mafita ba..
Shiru sukai ganin Kamal din ya shigo koh bud’e kofa basu ji ba.
Da kallo ya bisu halamun kamar yaji zancen su.
Kai ta d’auke tana turo baki,yayin da Muneera ta duk’ar da kai tare da fad’in
“Ina wuni ya Kamal..
Fuska ya sake tare da amsawa yana fad’in ya gida?
D’aki ya shige ya bar Deeja da harara cikin duhu.
Kai Muneeran ta girgiza,
“Ba koh sannu da zuwa,wallahi ki sauya halin ki,ki guji ranar da zai gaji ya auro miki wata,gashi ni neman tsayayye nake na rasa ki fa gode Allah..
Banza tai mata kawai tana tunanin wani abu.
Kira ya mata,dan haka tana chunno baki ta tashi ta nufi d’akin.
Ido ya sa mata,tamkar dabi’a haka wannan shegen chunno bakin ya zame mata wanda yafi tsana shi kam,dan haka cike da shan mur ya harareta.
“Ina abinci na?
Rai ta had’e tare da rike k’ugu tana gunguni.
A ganinta wannan ai gadara ce,a zuciyarta ta ce wai ‘ina abinci na? Toh ban dafa ba..
“Da ke nake.
Juya wa tai tana bubbuga k’afa da kunkuni tai waje,dan haka da kallo kawai ya bita had’i da furzar da iska.
Deeja kam halinta sai ita,da ya toshe nan zata 6ullo ta chan,gaba d’aya ta dagula mishi lissafi da duk wani tanadinshi a gidan aurenshi.
Kai kad’a, gab yake da ya d’au matakin farko dan saita tunaninta..
Da ido ya bita ganin ta shigo rike da faranti a hannu da abinci bisa kanshi har lokacin bakin nan a d’ane.
Sakkowa yai tare da zama,dan haka sai ta kawo da zummar ajiye wa ya damko hannunta.
Kokawar kwacewa ta hau yi tana nishi jin kam ya riketa kawai sai ta sau mishi kuka.
Baki ya saka, tun ma kamin ya kwad’e bakin shine zata mishi 6aci?
“Mey yasa a gaban kowa sai ki nemi nunan ban isa bane Deeja?
Kukan gaske ta fara,tare da fad’in
“Saboda bana sonka ni,sannan ka sani *INA DA BURI* wanda kai ba zaka ta6a iya cika min shi ba,dan haka ka sallameni na samo mai sona..
Ido ya zuba mata rai 6ace,kan daga bisani ya sau mata hannun tare da tashi.
Da sauri ta cigaba da binshi da fad’in
“Koh kashe ni za kayi wallahi sai na fad’i dan dole nake zaune da kai,amma ka ki ka gane..
Waje yai ya batta nan tana kunjin kuka,tabbas Deeja bata sonshi, hasashen zuciyarshi kam yau ya karyata shi.
Da kallo Muneera ta bishi cike da bakin cikin halin kawarta.
Tsaki tai mata tare da zarar jakarta ta fuce itama a gidan,dan haka tuni ta kara jiniyar kukan nata a ganinta ba wanda zai gane inda ta dosa,kowa bai kaunarta.
SAFHA…✍🏾
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
16_Glass din motar ta kwankwasa ganin ya jingina kanshi a jikin motar,a hankali ya zuge tare da kallonta yana k’ak’alo murmushi.
“Dan Allah kai hak’uri, nasan wataran zata daina.
Murmushi ya yi tare da kad’a kai,da ace Deeja na da hali irin na Muneera tabbas da yaji dad’in aurenshi.
A kance wai aboki na kwafar halin abokinshi toh tabbas Deeja bata kwafa ba,matuka yana son mace marar hargowa da ladabi had’i ga tarbiya.
Ba daban a gabanshi Deeja ta tashi ba, toh tabbas zai ce ba rainon Mamy ba ce.
“Ba komai Muneera,ba dai har kin fito ba?
Kai ta kad’a,
“Eh tafiya zanyi.
Motar ya bud’e mata tare da fad’in
“Shigo toh na sauke ki,dan hanyar gidan zanyi.
Jim tai tare da kad’a kai ta zaga bangaren da ya bud’e mata su na tafe su na tad’in Deejan.
Sai chan dare kusan goma ya shigo,lokacin tana zaune a parlour ta cika ta 6atse.
Koh ta kanta bai bi ba ya shige d’aki bai da walwala shima.
Tun daga ranar ya sauya mata,zai wuya taga fara’ar shi kullum a dunkume, baki ta ta6e,a ganinta wai tafi nono fari.
Kusan wata guda bai shiga sabgarta,iyakarshi da ita ido,in ta ga dama ta bashi abinci yaci,in abin ya motsa ta hana shi,dan haka shiga kitchen bai mishi wahala ya girka yaci ya fuce.
****
Tsam tai a band’aki tana wanka tare da saka kunne ta kofar band’akin jin yana dariya kasa-kasa.
“Oh no dorling, believe me,a satin nan kad’ai kin sanya na zurmada yawa…
Shiru yai halamun saurare,chan taji ya sake wata munafukar dariya cikin wani salo na so tare da fad’in
“I tell you..
Dariya ya sake yi,
“Ok,bari na duba zuwa gobe,Insha-Allah ki share min hanya…
A masife ta bud’e kofar band’akin ta fito tana huci daga ita sai towel.
Ido ya sa mata yana murmushi halamun yana sauraren ta wayar.
“Baby bani minti biyu zan kira..
Dariya ya danyi tare da kashe wayar yaci kunu kamar bashi yanzu yake dariya ba.
“Ni fa wallahi bazan d’au wannan wulakancin ba da rainin hankali,ban hanaka waya da koma wacce shegiyar bace amma ka yi a waje,banda cikin d’akina kuma bisa kan gadona…
Ido ya sa mata ganin wani karfin hali wai *Sadaka da d’an kishiya*.
“Ke a wa toh?
K’ugu ta kama tare da fad’in
“Oho,ni dai na fad’a maka,na daga ma k’afa amma naga abin sai gaba yake sake yi,ban hanaka ba,balle ka ce kishin ka nake,amma kai a waje.
Magana zai yi sai yai shiru tare da duba waya jin sako ya shigo,bud’ewa yai.
A hankali fuskarshi ta washe da murmushi.
Tuni ya sauka a gadon tare da fita yana reply ga text din da ya shigo ya batta nan tsaye.
Da harara ta bishi tare da ta6e baki.
Wannan dabi’a da Kamal ya koyo ta waya da budurwa ba karamin ci mata tuwo a kwarya take ba,tabbas ba kishi take ba,a’a, bakin cikinta d’aya da ita bai rabu da ita ta samo mai sonta da mutuwa a kanta ba kamar yadda taci buri.
Kwafa tai tare da k’arkad’e shimfid’a,dole yau ayita ta kare,sam bazata sa6u ba wai bindiga a ruwa,yau dole ya san yadda zai da ita.
Bargo taja jin an fara ruwa amma yana chan parlour har ta gaji da jiranshi.
Da harara ta bishi tare da d’auke kai,hararar shima ya bita dashi tare da ajiye wayar yana cire kayanshi,wanka ya shige bai bi koh ta kanta ba.
Bargon ta yaye tare da tashi ta d’au wayar ta shiga cikin chart nasun wanda network ya d’auke dole suka hak’ura ya dawo d’aki.
Tsaki taja ganin yadda yake zuba mata kalami tamkar wani na gaske budurwar na aiko mishi da kiss,maganar turo magabata yake network din ya d’auke.
Wayar ta ajiye jin zai fito tana aika mishi harara.
Jiki ya goge da towel yana yar waka irinta masoya.
“Bari kaji da wai,wannan ba shi zai sauya min Buri ba,wallahi in kaso ka auro hud’u amma in na fuce,dan fa dole ka sallameni nima na samo nawa masoyin..
Towel din ya ajiye yana jinta tare da fesa body spray yana murmushi.
Juyo wa yai daga shi sai wandon ball iya gwiwa tare da hayo wa gadon yana kallonta wani iri.
Bargo yaja yai mata banza,dan haka tuni ta kara kulewa ta hau bala’i wanda ya jima baijishi ba.
Tashi yai tare da zama ya jingina pillow ya sata a gaba kamar TV.
Bakin ya kalla sam koh coma batai balle ta sanya full stop a masifar duk rabi akan sai fa ya sallameta itama ta samo saurayinta mai sonta.
Bak’in yai saurin toshe wa da nashi tare da janyota gareshi ya kashe maganar.
Yau kam a gaske ya tura ta bango,dan haka dakyar ya saito da tuaninta ta sauke taurin kai tare bin ra’ayin zuciyarta kamin tai surrender.
Yafi kowa sanin alkibilar da Deeja dosa,dan haka cikin ruwan sanyi yake kashe bakin tsanyar.
Kuka take mishi tsakaninta da Allah bayan komai ya lafa, kam ya riketa yaki sakarta, dan haka cikin sassanyar iskar daminar had’i da sanyin ruwan dake busowa bacci yai awun gaba da ita a haka tana mitar ya cuceta.
Kai ya girgiza yana murmushi, bai jin zai iya rabuwa da Deeja duk rintsi kuwa,amma hakan bazai hana ya samu saukin rayuwa ba,dan haka ya riga da ya gama shawarar abin yi duk kuwa da yasan zai sa Deejan a tsaka mai wuya.
Dan haka akanta bazai hana zuciyarshi abinda tai niya ba koh da kuwa gangar jikinshi bata so.
Bakin yaja kad’an tare da fad’in
“Ni da ke ai takalmin kaza ne,in an mutu sai a raba, ki shirya kar6an haka.
Bargo yaja musu tare da gyara kwanciya yana jin saukar ajiyar zuciyarta.
Kai ya girgiza, a kullum ana kirarin ba’a sonshi amma hakan bai ki a lafe mishi jiki ba koh da kuwa ya sauta, matuka yana mamakin kalar rigima irinta Deejan shi.
Hannu ya kai tare da dungure mata kai a hankali yana dariya,cikin baccin ta chunno baki tare da dan motsa wa, kai ya kad’a, yanzu ya yarda a jininta abin yake.
SAFHA…✍🏾
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
©SAFHA
SADY JEGAL
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSAT ISMAIL (MMN HANEEF)
17_Jiki ya zare a hankali jin ana kiran sallah sai kwa warai! Ta bud’e ido tare da sauke shi bisa kanshi ciri da tuhuma.
Yake yai mata,dan haka tuni ta sau kuka tana tatta6e baki kamar na shagwa6a66un yara tana shusshura k’afa wanda ya sanya shi sauka da sauri yana dariyar keta ya shige band’aki ganin ta rarumo pillow.
Lalle kam Deeja ta iya salo na nad’e taburmar kunya,yanzun zata nutsu ta amshi messages daga baya ta hau mishi bori,sai dai yau yasan sai ya toshe kunne dan mita, dan dama shi din mai laifi ne.
****
Soyayya tsantsa Kamal ke zubawa da budurwarshi wacce yake nuna ma Deeja yadda yake sonta tamkar ranshi.
Ya daina waya da ita a d’aki, koh ta kira koh shi ya kira sai ya fita parlour dan gudun masifar Deeja.
Sam ita ba wayarshi ba ce take bata haushi sama da yadda yaki zuciya ya sallameta.
Kwance yake saman kujera yana waya yana murmushi wanda daka nufo gunshi zaka fahimci tsabar walwala kwance a fuskarshi.
A kanshi ta tsaya rike da k’ugu tana hura hanci.
Ido ya sa mata tare da fad’in
“Bari zan kira ki..
Harara ya sau mata tare da kashe wayar saboda gudun kar ta kwafsa mashi.
Tashi yai tare da zama yana latsa waya tare da fad’in
“Ya aka yi?
Baki ta ta6e tare da fad’in
“Ina zancen mu ya kwana? Dan kasan Allah? Toh na gaji.
Kai ta d’auke tana jijjiga rike da k’ugu.
Murmushi yai tare da jingina da kujerar yana kallonta.
“Toh ya ki ke so ayi?
A fusace ta ce
“Ka sallame ni kawai..
Ido ya sa mata hannu bisa ha6a.
“Shine matsalar?
Kai ta jijjiga da sauri
“Kwarai kuwa.
“Toh bazan sallama ba,sai mey kuma?
A zabure ta sau kugun tare da fad’in
“Ai kwa yau baka isa ba,dan bazan ta6a zama naga shirmen auren nan naka ba,bayan na tafi ka auro dubu chan ta matse ka bani ba.
Murmushi ya yi tare girgizaKai.
“D’aya ma ta ishe ni rayuwa, amma dole ki zama ‘yar kallo,dan fa bazan saki ba,aure kuma ba fashi.
Daga hakan ya tashi yana latsar waya ya barta gurin tsaye tana huci tamkar namijin zaki.
***
Bayan kwana biyu abubuwa sun k’ara jagulewa tsakanin Kamal da Deeja, kowa ya fita sabgar wani sai dai Deeja na da bak’in cikin abinda Kamal ke yi mata wanda take ganin tsabar mugunta ce.
Da shirinshi ya fito na fita office ta tareshi tana masifar sai fa ya sallameta,dan jiya har tai bacci tana jiyo sautin dariyarshi.
“Kar ki 6atamin rai don Allah, saboda ina so na fita cikin farin ciki da annuri fuska na min walwali dan so nake in fara tozali da sahibata, Ok?…
Baki ta saka tana kallonshi,dan haka sai ya ware mata yatsunshi biyu tare da karkatar da kai ya ce
“Bye-bye..
Daga hakan ya ra6a ta gefenta ya fice daga gidan yana dariyar mugunta.
Wani irin bak’in ciki ne ya k’ara rufeta wanda yasa ta kai zaune bata shirya ba ta sau kuka.
Ba dan tuno da zancen Abba da yau ta tafka rashin mutunci tai gida.
Gidan Maman Ihsan ta shiga,ita kad’ai take ganin zata iya fad’i ma kukanta, duk da koh shawarar ta bata ba lalle ta dauka ba.
Ajiyar zuciya Maman Ihsan din tayi bayan ta gama saurarenta.
“Wannan ranar nake guje miki a kullum Deeja,sai dai ke abinda ke gaba gareki kawai ki ke yi,yanzu ne zaki rintse ido,dan fa zaki ga abu iri-iri.
Baki ta ta6e
“Ni fa ba kishi nake ba,burina kawai ya sallameni.
Ido ta sa mata,ta ma rasa mey zata fad’a mata,dan haka ido kawai ta sa mata karshe dai da fad’a suka rabu.
Yinin ranar ko abinda zata ci bata tashi ta nema ba har Kamal ya dawo daga gurin aiki tana kunci.
Da sallama ya shigo yana yar waka,dan haka da harara ta bishi,daga shi har sallamar ta watsar su gefe.
D’aki ya shiga ya rage kayan jikinshi sannan ya fad’a kitchen saboda ganin gurin cin abinci wayam alamar bata girka ba yau.
Girkinshi yake yi hankali kwance yana waya had’e da murmushi cikin aminci rike da serving spoon.
Kwafa tayi tare da kunna tv amma har lokacin tana tsintar firarshi hankali kwance cikin ‘husky voice’.
“Kinga ai dole na shiga kitchen na girka tunda bani da mai yi min, sai dai nasan cewa daga ranar da kika shigo gidan nan ko spoon ba zan k’ara rik’ewa ba ballantana shiga kitchen girki”…
Dariya ya danyi tare da fad’in
“Of course dorling.
Dariya ya kyalkyale da ita,dan haka da sauri ta makawa kitchen din harara.
Tashi tai tare da isa kitchen d’in ta bud’e fridge ya dan juyo like da waya a kunne.
Harara ta sau mishi tare da tsiyaya ruwa a cup,dan haka sai ya juya tare da kok’arin juya abincin shi yana fad’in
“You know, when we’re together I can truly be myself, and that makes all the difference….
Kinsan dalili?
Ruwan take kur6a tare da kasa kunne tana kwankwada.
Jim yai tare da yin y’ar dariya halamun saurare tare da fad’in “Eh man,cos you’re are the girl of my dream,and I love yo..
Ruwan ta sauke tare da fara tari halamun ta kware jin wannan kalmomi.
Wayar ya cire a kunne tare da juyo wa yana kallonta, baki ta chunno tare da rufe fridge din da dan karfi taja tsaki ta fuce.
Wayarshi ya cigaba da yi ya batta da sintiri daga d’aki zuwa parlour.
Hakan ya gama ya tu6e ya shiga wanka, inda hankalin Deeja ya gaza kwanciya,yau dole ta takawa shegiyar nan birki domin taji ita ta kira,dan haka ta tashi ta d’auki wayar tare da duba last call nashi ta duba.
Cikin sauri ta d’auko wayarta tana kwashe lambar tana sakawa a tata wayar da niyyar kiran kowace ta ci mata zarafi,su kare a waje amma banda cikin gidanta.
Tana saka lambar tana ganin sunan Muneerat na appearing, idonta ta fara murzawa sannan ta k’ara duba lambar tana k’ara sakawa, again Muneerat ta gani.
Wani irin uban ihu ta kurma wanda ya fitar da Kamal daga toilet d’aure da towel a k’ugunshi yana fad’in
“Lafiya?
SAFHA…✍🏻
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
©SAFHA
SADY JEGAL
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSAT ISMAIL (MMN HANEEF)
( _Muna mik’a sak’on godiya gareku masoya littafin *INA DA BURI*, sak’onku na zuwa muna a kowane lokaci, mun gode Allah yabar k’auna, SAFHA na gaida Ku all👌🏾_)
18_Ganin wayarshi a hannunta ne yasa ya karasa tare da warce wa ganin tana digar da kwalla tare da kallon wayar.
Ido ta dago tare da kallonshi,da sauri ta ce
“Munafuki,mayaudari, maha’inci, azzalumi kawai…
Ido ya waro tare da bud’e baki.
“Yanzu ace duk duniyar nan ka rasa wa zaka aura sai makusanciyata? K’awata?
Shiru yai nashi ido,dan haka sai ta cigaba.
“Lallai na ya yarda da d’a namiji munafuki ne.
Ita kuma munafukar ashe shi yasa kwana biyu ta d’auke k’afa 6at! Da zuwa ashe cin amana ake kulluamin..Toh wallahi sai ta gane shayi ruwa ne dan ub..
“Ke! Maintain wallahi..
A zabure ta ce
“Bazan yi ba,munafuki kawai algungumi.. Toh yau dubunka ta cika..
Rai ya had’e
“Kar fa ki nemi rainan hankali, dan ina da right na neman matar da ta dace da rayuwata,na duba kaf banga kamar Muneera ba…
“Karya ne wallahi, dan kuwa baya kaci ba gaba ba,da har ka kare a wacce nafi kyau da fasali,shegiya mummuna kawai..
Dariya yasa harda kyakkyatawa
“Eh a haka nake son abata tamkar na zauce.
“Kuma ke ki ka gano muninta,amma ni a gareni she’s gorgeous,dan banga amfanin kyaun d’an micijiji ba,kyau ba kyan hali..
Ido ta sa mishi,
“Ka fito ka ce bani da kyaun hali kawai,amma haka ai ka gagara sallamata dan naci,yanzun ma ba zama zanyi ba,wallahi gidan mu zani..
Kayanta ta shiga had’awa tana mai zubarda hawaye tamkar famfo tana surfawa Muneerat tofin Allah tsine.
Kaya yai saurin zirawa ganin da gaske take tafiya zatai.
“Kar ki fita daga gidan nan..
“Sai na fita,in yaso ka jika gidan ka kora da ruwa,amma sai na tafi,daga baya ka biyoni da takkada ta..
Yin duniya taki ta tsaya dan haka sai ya kullo gidan ganin ta tari Napep ta hau yabi bayanta.
Kuka reras ya tarar tana yi tare da tsarawa Mamy abinda ya faru, ga chan mey Napep a waje sai masifa yake ba’a biyashi ba.
Koma wa yai tare da sallamarshi ya dawo gidan.
Waje ya samu ya zauna tare da gaida Mamyn ta amsa.
Magana zai yi Mamyn ta ce yai shiru tana zuwa.
Sama tayi d’akin Abba,dan haka sai yai kwafa.
“Lalle kin kawo kuka gidan mutuwa,dan kin san da kowa ya gaji da halin ki a gidan nan ni kadai nake iya maleji da ke..
Harara ta kwad’a mishi ido yai jajur,kamin tai magana sai ga nan Mamy ta sakko.
Iya had’e rai Mamy tayi har ta tsorata da ganin yanayin nata,dole ta kara jiniyar kukan nata ganin dakyar ta samu nasara.
“Ki tashi bakin ki alekum ki 6ace min da gani,ki kuma tabbatar da d’akin mijinki ki ka koma in dai kin yarda ni din ni na haifeki..
Gwiwa biyu ta zube halamun roko.
“Mamy k’awata fa zai auro..
Da sauri ta ce
“Koh ‘yar uwar ki ce sai kin koma,ka min dai dai wallahi Kamal,ki kuma ji da wai ni na goya mishi baya ya auro ta..
Kukan ta bari tare da kallo Mamy baki sake.
“Mamy kina sona kuwa?
Kai ta girgiza
“Bana sonki,dan kin san ni bana shiri da mai shegen taurin kai,kowa yasan irin zaman da ki ke a cikin gidan ai mun zuba miki ido.
Sabon kuka ta saka ganin Abba na sakkowa, tasan dole karan nan ya goya mata baya.
Zama yai kawai yana mai sauraren kukan nata,sai da ta tsagaita ya ce
“Ya mukai da ke lokacin tariyarki?
Shiru tai tana jan zuciya.
“Toh har yanzu sharad’ina na nan,in har ki ka kaso aurenki wallahi Khadija bani ba ke,zance na karshe kenan,ruwan ki kibi mijinki koh kisan inda dare ya miki..
Rigarshi ya k’arkad’e tare da fita ya batta da kukan kiran Abba.
Haka tana ji tana gani ta koma dan yadda ran Abba ya 6aci tsaf tasan zai sallamata,dan haka dole tazo tai yakin ita kad’ai.
Ba shiri ya fita dan yadda take sauke mishi ruwan bala’i cikin kuka,shi har tausayi ma ta fara bashi,amma fa ba shi zai hana abinda yai niya ba.
****
“A gaskiya ki sauya tsari Deeja,ina fa jiyo muryar ki sama da ta mijinki kuna ka ce na ce wannan sam ba halin kwarai bane,wallahi zaki sha wuya randa zai gaji da halinki ya auro wata..
Hawaye ta goge,hamuryarta ta dashe dan kukan da tasha daga safe zuwa daren yau.
Zama ta gyara tare fad’in
“Na nawa kuma…
Da rashin fahimta ta kallota,
“Ban gane ba?
Wani hawayen ne ya sake zilalowa,dan haka murya na rawa ta fara magana.
“Aure zaiyi,amma wallahi karyar kuturu tai kadan balle ta makaho,yaje gida ya kalamence su,yau naga warewar launi ta fata,ni Deeja kowa ya tsane ni,a ciki harda k’awata aminiya..
Kuka ta sa,dan haka baki sake take kallonta dan bata fahimci inda ta dosa ba.
Shin kishi take da auren koh mey?
Koh kuwa ta fara son Kamal har kishi yasa ta fara hauka haka da surutai?
SAFHA…..✍🏻
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
19_ “Ban fa gane inda ki ka nufa ba?
Yadda abin yake ta sanarta,dan haka baki kawai ta saka tana kallonta,tasan makamancin haka zai iya faruwa da Deeja,amma koh ita taji shocked da taji k’awarta yake nema.
Ido ta rintse tare da matso kwallar dake idonta ta zubo kuncinta,dan haka tuni sai ta fara bata tausayi.
“Tabbas anci amana ta,Insha-Allah kuma Muneera sai taga karshen cin amana,dan zata gwammaci da kid’a gwara karatu,mu zuba ni koh su..
Harara ta sau mata.
“Ki ajiye cika baki yanzu ki hau gyaran dabi’unki,sauran abin ki tsimayeni gobe zan zo dan yanzu Abban Ihsan zai dawo,dabara ta rage gare ki,walau ki sauya hali koh yanzu ki ka fara ganin tasku.
Tashi tai ta tafi tana mata sai da safe,da kallo kawai ta bita hawaye na zuba.
Tabbas bata son Kamal,amma wani tokararren d’aci ke tokare makoshinta mud’in ta tuno da zai aure,auren ma da Muneera.
Kai ta gyad’a, dan haka sai ta bi zancen Maman Ihsan na dabara ta rage nata,dan haka hawaye ta goge tare da fad’awa wanka dan wanke hawayen.
Da sand’a ya shigo gidan har wata fad’uwar gaba yake dan tuna da bala’in da ya fita ya batta tana yi bai san da wacce zata tare shi ba.
Kai ta dago jin bud’e kofar ta zuba mishi ido,dan haka da sauri ya sha mur tare da d’auke kai ya shige d’aki yana furzar da iska.
Har ya fito a wanka bata shigo ba,ganin yaci abinci kawai sai yabi lafiyar gado tare da d’akko waya tare da fara dailing ta shigo da sauri ya sauya maganar zuwa ta soyayya har wani lumlumshe ido yake.
Baki ta ta6e tare da yin wajen kamar mai shirin kwanciya ta warce wayar ta zuba waje da gudu.
Biyota yai lokacin tana surfa bala’i.
“Shegiya wacce ta rasa mashinshini a gari ai dole ki koma kwatar mazan jama’a, karya kawai shasha maciji da baka ramin k’anka sai na wasu,toh wallahi baki isa ba dan kinyi kad’an..
Baya tai ganin ya taho,dan haka sai ya tsaya tare da fad’in
”Ki bani wayata..
Da sauri ta ce
“Bazan bayar ba din,wallahi sai na ci ubanta tukunna..
“Auxubillah… Ke fa ina ga notin kanki ya since?..
Kai ta gyad’a tare da yin bayan kujera.
“Ai kasan daga turu na fito.. Ke kuma bari kiji,in har kin cika Muneera ki yarda mu had’a ido dake,wallahi sai na lahira ya fiki kwanciyar hankali, karya ka…
Ritsata yai a bayan kujerar tare da kai ma wayar chafka ta rike kam.
“Ki ban wayata..
“Wallahi bazan bayarba..
Hannunta d’ayan ya murd’e marar wayar,dan haka batai wata-wata ba ta dakarkare ta makata wayar da kasa tana huci.
Da ido yabi wayar,kan da sauri ya cikata ya nufin gun wayar da tai filla-filla ya hau tattare wa.
Kai ya dago yana muzurai.
“Ni ki ka fasawa waya?
Zani ta tattare tare da chunno baki.
“Eh din na fasa,a gaba ka sake hawa gadona kana waya da wata she..
Na kare taci ganin ya yo kanta,ganin kan ta isa d’aki zai iya cinmata yasa suka hau zagaye parlourn da gudu har lokacin bakinta bai mutu.
Huci suke gaba d’aya na gajiya su na kallon juna had’i da maida numfashin gajiyar da sukai na tsere amma ya kasa kamata.
“Ai dama na fad’a maka duk ranar da zaka sake min waya da wata ‘yar katuwa a d’aki zan d’au mataki..
“Ba dai ni ki ka fasa wa waya ba?
K’ugu ta rike tare chunno baki,dan haka sai ya jijjiga kai.
“Wannan ba zai sauya komai ba daga kaunata da Muneera ba ki san wannan.
“Oho dai,waya ce kuma na fasa..
Hannu ta tafa harda su murgud’a baki tana fari da ido irin na sarakan iya tsiwa.
Tsalle d’aya ya buga ya isa ga bayan kujera dan haka da sauri ta zille ta nufi d’aki tana ihun wayyo Mamy a taimaketa ganin ya biyo ta da gudu.
Bayan gida ta shige tare da kok’arin rufe wa ya danno kai tare da sa sakata.
Baya tai chan jikin shower ta kulle tare da marairace fuska ganin yana tattare hannun rigarshi,dan haka cike da marairaita ta hau fad’in
“Dan Allah kai hak’uri na tuba.
Murmushin mugunta yai yana matsowa.
“Ba ni ki ka fasawa waya ba?
Kai ta girgiza da sauri tana sake makuruwa jikin bangon har yai mata dabaibayi,dan haka da sauri ta rintse ido kawai ta sadakar jibgarta ma zaiyi.
Dan haka bakinta kad’ai ke furta
“Na tuba..
Ido damk’e kam.
Ido ya zuba mata,sai shegiyar tsiwa ga iya tsoro kuma,bakin ya kalla,yau kam karya take tace mishi wannan ba kishin shi bane kwance fuskarta yake gani har kawo ga fasa waya.
Kai ya daga ganin shower kawai ya murd’a ta zubo kanta bata zata ba,dan haka jin sanyin ruwan da sauri ta zabura ta kankamoshi tana jan zuciya.
Dan kwali ya fara zamewa,dan haka sai ta dago kai tana dan ta6e baki kamar zata sau kuka.
Hannu ya kai bisa bak’inshi tare da fad’in
“Shhhh..
Halamun ta rufe mishi baki.
Kukan ta had’iye tare da turo baki gaba,da sannu cikin iya sarrafa fitinar Deeja abin ya wuce ga wankan gaske,da zatai magana zai sa hannu a baki halamun tai shiru,ranar taga salon da bata ta6a tunanin Kamal zai iya shi ba,har Allah-Allah take su dauwama a hakan.
Zo ka ga wai yau su Deeja ne da kunya,sai sissinke kai take kasa-kasa,yau d’aya yasa ta fara tunanin sauya Buri, sosai ta yarda da Kamal namijin duniya ne.
Dago da kai tayi lokacin da yake goge jikinshi jikin mirror,kai tai kasa dashi ganin ya hararota kad’an.
Kirar karfafan maza gareshi,irin dai kirar da take bida dan taki jinin sokon namiji mai kirar mata jiki a sake.
Kai zata iya fad’in yana da duk wasu qualities da su Aminu su ka rasa a baya illa abu d’aya..
Jim tayi, dan a yau ta karyata abu d’ayan nan,dan yanzu kad’ai taga gundarin salon so gun Kamal wanda har yasata taji kunya.
Baki ta chunno gaba tuno da yadda yake zuba ma Muneera kalam na tsantsar so da kauna,a ganinta ita ya dace yai ma,ita ta chanchanci jinsu ba wata chan Muneera ba..
Ido ta k’arkad’e tare da d’auke kai a kallonshi ta tur6une fuska tare da fad’in
“Deeja dawo hankalinki ki saita tunanin ki..
“Ya akai Deeja dorling? Uwar gida sarautar mata..
Fuska ta yamutse tamkar taji abin ki.
Wai uwar gida? How boring..
Dan haka harara ta sau mishi tare da kulewa cikin bargo.
Kai ya girgiza, lalle yaro man kaza,da sannu ya fara saita tunanin kwanyar Deeja.
Kai ya rausayar tare da fad’in
”Hooo ni Kamalu..Ni kad’ai ma gayya ce guda.
A hankali.
SAFHA…✍🏾
[4/4, 6:51 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
20_Washegari Maman Ihsan ta shigo jin Kamal din bai fita ba tasan yau week end.
Su na zaune Kamal din ya fito zai tafi.
Bayan sun gaisa zai wuce ta zunguri Deejan dan haka da sauri tabi bayanshi dan tambayarshi fita kamar yadda ta ce tayi.
A dan zaman su sosai ya fuskanci Maman Ihsan mai son zaman lafiyar su ne,dan haka yake maraba da zuwanta a kullum.
Gyale kawai ta d’auka su ka fuce tare da tarar Napep.
A wani kofar gida suka tsaya tare da sallamar mai Napep.
“Ina muka zo?
Hannunta ta kamo,
“Ke dai muje kar ki ce komai..
Ciki su ka shige, sai kwa akai sa’a mijin na gidan,dan haka tun tsoma kafarsu su ka fara jiyo hayaniya halamun gidan ba lafiya.
“Kullum magana d’aya zanyi ki rika daga min murya tamkar wani d’anki,ba ta yadda za ai muyi sati ba tare da makota sun jiyo ba,
na fa gaji da halinki, gab nake da na d’au mataki..
“Ni kuma na gaji da kai,dan a kullum baka kaunar zaman lafiya,abu kad’an zaka fara mita kamar wani tsoho akan abinda bai kai ya kawo ba..
“Ba zaki daina min ihu?
“Eh bazan daina ba,wani irin zama ne wannan, ni wallahi na gaji..
Maman Ihsan ta kallo ido ware.
“Koh dai mu koma?
Kai ta girgiza mata,
“Ai dan wannan na kawo ki,na gode Allah da muka tarar da haka,dashi zan baki darasin farko..
Shiru sukai ganin mai gidan ya fito a fusace yana huci amma duk da haka matar ta biyo shi tana fad’in
“Kai ne kaddara wallahi ba aure na ba,samari nawa na ture na aureka? Kuma wallahi ni ba marar kunya ba…
Shiru tai ganin su Deeja na kallota,koh ta kansu bai bi ba ya fuce dan fa ta kunno shi.
Yawu Deejan ta had’iye tana waro ido, sam bata ji dad’i ba,ashe haka fad’a da namiji yake bai da dad’in ji balle gani?
Wayancewa matar gidan tayi had’i da sosa keya cike da kunya.
“Bissmillahn ku..
Yak’e Maman Ihsan din tayi tare da fad’in
“Sannu Ummi..
Tasan gatse tai mata,dan haka sai tai shiru.
“Har yanzu kuna nan da hali koh?
Kuka ta sa ma Maman Ihsan din bayan sun zauna.
“Wallahi na gaji da auren nan,aure koh na kiyayya albarka, kullum rashin jituwa muke tamkar wasu makiyan juna?
“Yanzu wa ye zai ta6a cewa Abbakar ya ta6a nuna min so a baya?
Kai ta girgiza.
“Babu,auren mu yafi kama da wacce aka lika mishi ni dan dole,dan haka na gaji,na gaji Zainab..
Murmushi tai tare da jijjiga kai.
“Ni dai har kullum ina mamakin ina dumbin wannan soyayyar da aka gina a baya taje? Ina wannan tattalin da mutunta juna yaje kamin ayi auren?
Kiyi wa kanki fad’a, shima yai kanshi ku gyara aurenku,dan kun fara tara iyali.
Shiru tai mata kawai tana kuka,har kullum in ta tuno baya koh ita tana karyata sune masoyan nan a baya wanda ake kiran su da ‘Love birds’ dan tsantsar son da suke gwada ma junan su.
Ita dai Deeja ta sai binsu take da ido,dan ita sam bata gani akasa ba,sannan wannan suna bai kamaci gidan nan ba na ‘love birds’.
Fad’a tai mata kamar kullum in tazo gidanta kamin su ka fito.
A kalla sun shiga gida kusan uku tukunna su ka dawo gida.
Ajiyar zuciya tayi,yau d’aya ta fahimci wani darasi duk da Maman Ihsan bata ce komai ba.
Zama ta gyara tare da kallon Deejan.
“In zaki karad’e garin nan Deeja toh za ki sha mamaki acikin gidan auren jama’a, kowa da matsalarshi,ba wai kuma dan babu soyayya ba.
Kai ta girgiza
“A’a, koh d’aya, wallahi zaman ne kawai bamu iya ba,abin da nake so ki fahimta soyayya ita kad’ai bata wanzar da farin ciki.
“Idan soyayya kad’ai ke gyara rayuwar aure Deeja nai imani ba mai jin kan Habu da Ummi,sunyi soyayya irin wacce ba kya zaton zasu iya.
Hakan yasa muka musu lakabi da sunan “Love birds” dan tsantsar so da tattali.
“A gare mu Ummi sunanta ‘Ta Habun’, yayin da Abbakar ake kiranshi ‘Na Ummi’.
Duk yadda zan kwatanta miki ba zaki gane ba,amma nasan a wachan lokacin Habu zai iya mutuwa akan Ummi,haka itama.
“Yanzu fa?
Kallonta tai tara da girgiza kai.
“Ba ta inda zai yu,tunda gashi a gaban ki kowa ya furta ya gaji da d’an uwanshi..
Kai ta jinjina tare da dukarwa.
“Dan haka Deeja soyayya ba koh mai bace a gidan aure mud’in ma’auratan ba su iya zaman ba.
“Kiyi kok’ari kiyi nazarin gidajen da muka shiga kad’ai, nai imani in zaki karad’e garin nan gida d’ai-d’ai ne akai aure ba soyayya, amma yanzu soyayyar an matsar ta gefe, an ari abubuwan nan an lullu6a mata
Hak’uri
Sadaukarwa
Tattali
Biyayya
Mutunta juna.
“Su ke haifar da iya zama,idan wannan suka shiga toh lokacin soyayya ke da tasiri a gidan auren ku.
Kinga kenan ashe soyayyar titi bata da wata fa’ida,ta gidan aure kad’ai ke da tasiri idan har kun iya zaman.
“Ina so ki zubda makaman yakinki ki amshi aurenki hannu biyu ki bashi daraja,ki koyi ladabi,da iya tauna harshe a gaban miji, yanzu ne zaki gina soyayyar da ki ke muradi ba wai a titi ba,mijinki yana kaunar ki,ga tattali,amma da halamun kin fara tsire mishi tunda ke baya gaban ki.
“Shin irin soyayyar su Ummi ki ke bid’ar ki samu koh wacce zata wanzar miki da durewar zaman lafiya?
Kiyi tunani Deeja,nasan a yau kin samo darasin rayuwa,ki ajiye *INA DA BURI* ki kama gyaran gidan ki,na tabbatar a gaba shima Burin zai baiyana.
“In kuwa ba haka ba,ki cigaba daga inda ki ka tsaya,akwai mata a gari wanda suke neman kamar Kamal ido bud’e sun rasa irin Muneera,nai imani da gudu zasu zo bauta mishi koh da baya son su..
“Kiyi tunani,sannan in kin kashe auren,shin kina da lasisin za ki samu saurayi mai jini ajika da zai kwashi bazawara har ya gwada mata irin son da ki ke da Burin?
“Ki tuna yanzu farashinki ya sauka,sannan zawarci tsada yake,ruwanki ki rike mijinki,ruwanki kar ki rike,ni dai nayi iya wanda zan iya,na kuma fita hakkin makotaka da ‘yan uwa a musulunci,na barki lafiya.
Da kallo ta bita har ta fuce kamin ta tsunduma tunani,ba zata ce ga ahalin da take ciki ba,abu d’aya ta sani ta zubda makaman yakinta daga yanzu zata gyara kuskuren da ta tafka,a shirye kuma take da ta sauya halinta,a shirye take da ta nuna ma Kamal lalle *Mata suna suka tara*
Ita Deeja ta fice tunaninshi,dole ta nuna mishi Muneera ba tsarar jerawarta bane.
Mike wa tayi tare da rike k’ugu, tamkar mai magana da wani ta fara masifa.
“Wallahi kinci karya kin kwana da yunwa Muneera,Kamal na Deeja ne ita kad’ai,daga yanzu zan nuna miki da banbanci.
Anya Deeja?
*Toh ayi dai mu gani in basilin zai soya kosai*😜.
SAFHA..✍🏾
[4/4, 6:52 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
21_Agogo ta kalla,shida saura an kusa kiran magriba kawai ta nufi kitchen.
Abincin mai rai da motsi ta d’aura wanda bata ta6a yin irinshi ba sai dai tai ma cikinta kamin ta wuce sallah ta sake koma wa.
Tsadadden flaks nata ta fito dasu har bayan isha’i tana abu d’aya.
Tsaf ta gama tare da jere su bisa center table akan faranti ta shige wanka.
Gashi ta sharce tare da zama gaban mirror tana kallon jeren kayan kwalliyar wanda bata ta6a bud’e wasu ba ma,iyakarta powder da mai.
Murmushi tai tare da gyad’a kai,dan haka sai ta gyara zama ta hau tazar gashi da kyali.
Mudubi ta d’auka bayan ga wani a gabanta tana duben tsaruwar da kwalliyar tayi sai wani turo baki take kamar zatai selfie,tabbas dole ya tantance tsakanin zare da abawa,a yau ita koh Muneera?
Sabbin kayan da ya ta6a kawo mata na riga da skirt ta dakko bayan ta tufke kan da ribbon cikin style.
Ainun ta kashe kyau,sai tsabar kamshi ke tashi ko’ina yai tsaf.
A yau take cikkakiyar matar gida,dan har su burner aka jona amma har tara da wani abu shiru ba Kamal.
Ta fa fara kulewa,kawai daurewa take,dan sai yanzu zuciya ta fara rayo mata tabbas in yai dare zance yake zuwa.
Kai komo ta fara a tsakanin parlourn, wani irin tsanar Muneera take ji a kasan ranta,ta aminta tsananin kishin Kamal take a yau,musamman in ta tuno kila yana chan yana watsa mata kalaman soyayya sai taji kamar ta zunduma ihu.
Kukan zuci take,ga ta fasa waya balle ta kira taji a inda yake har wannan lokacin, yau d’aya ta damu da rashin dawowarshi gida.
Kwafa tai tana kallon agogo,9:32pm,kai ta jijjiga tare da tsiyaya ruwa a kitchen koh ta ji saukin wani abin.
Da sallama ya shigo had’i da wakar
_’Rai da Buri,duniya kuma labari’_
Da cup ta fito a hannu da sauri tana kallonshi da tuhuma.
Chak! Yaja ya tsaya tare da barin wakar yana dubenta daga kasa har tsakar kai baki sake..
Matuka tai kyau,irin kyaun da bai ma tunanin ta iya ba,gidan ya kalla,tabbas akwai sauyi a yau daga ita har gidan,lalle ne wanda yaki sharar masallaci zai ta kasuwa, dan haka dariya ya fara neman kunshe,yayinda ta had’e rai maimakon ta tar6o shi kishi ya hana,sai ma fad’in
“Daga ina ka ke?
Dariyar ya had’iye tare da saita kanshi cike da mamaki,yau ce rana ta farko da yai dare ta tambayi daga ina yake,kai ya jijjiga, lalle kwalliya ta fara biyan kud’in sabulu.
“Daga zan..
Shiru yai jin Nokia da ya siyo mai torchlight na kara halamun an kira.
Kai ya dago tare da kallota,dan haka sai ta tabbatar da zarginta Muneera ce.
Kofin ta ajiye tare da isa jin ya d’auka ta kai hannu zata warci wayar ya kauce tare da hararota,bata daddara ba ta sake kai wa wayar chafka tana zunguro baki ya ruko hannun.
“Toh Abba..
Jin ya ce Abba yasa ta dan tsaya had’i da kasa kunne.
“Ok,Insha-Allah goben zan kai shi..
Sallama sukai cike da girmamawa tukunna ya sauke wayar yana aiko mata da harara.
“Wai mey ke damunki ne?
Baki ta chunno tare da kok’arin kwacewa jin ya matso hannun.
“Bar fa ganin na kyaleki jiya in ki ka sake fasan waya zan dau mataki ne..
Kalloshi tai tare da sake d’ane baki.
“In dai naji kana waya da wata ‘yar katuwa a turmi ma zan dakata
kowa ya huta..
Hannun ya cika yana kwafa,dan haka kawai sai ta kai hannu kan kayan hannunshi ta amsa tare da da yin gaba tana kunkuni.
Da kallo ya bita baki a sake,tabbas da sauyi a gidanshi ba kad’an ba,koh da tsiwar yau hankali ya dira tsakar kan Deeja kad’an, amma dole ya zuba ido dan ganin kamun ludayinta.
Kan center table ya kalla ganin jere da flaks,dariya ya kunshe ganin ta shige kitchen ya nufi d’aki yana jijjiga kai.
D’akin ta biyo shi,dan haka sai ya juyo jin ta rufe kofa bata karaso ba.
A jingine take jikin kofar tana dubenshi,bai 6arke da lamarin ba sai da yaji ta ce
“Sannu da zuwa..
Ido ya sa mata baki sake.
“Mey ki ka ce?
Ba musu ta sake fad’in
“Sannu da zuwa na ce.
Kai ya jijjiga tare da cigaba da abinda yake,dan haka sai ta fuce dan zuba mishi abinci.
Parlourn ya fito rike da laptop da waya a hannu ya nemi waje ya zauna.
Abincin ta tura mishi a hankali tare da koma wa ta zauna.
Kallonta ya sata,kawai sai yai kamar bai ga ba ya fara latse-latsen system.
“Abincin naka zai huce fa..
Kai ya dago tare da sa mata ido.
“Nawa?
Kai ta jijjiga tana d’an 6ata fuska gudun kar yai mata gori.
Murmushi yai tare da jijjiga kai.
“In tambaye ki man..
Juyo wa tai tare da kafeshe da ido,dan haka sai ya cigaba.
“Hope ba wai cin hanci ke ki bani ba?
Baki ta saka tare da mishi kir! Da ido.
“Dan in shine toh ki sani ba abinda zai sauya akan niyata,gwara ma kiyi dan Allah kila ki samo lada…
Galala take kallonshi ganin ya cigaba da abinda yake.
“Tabdijam! Toh wallahi sai ka ci,dan bazan shiga kitchen tsawan awa ta uku da rabi a tsaye ba kazo ka ce ba zaka ci ba,aure kuma ban hanaka ba,dan ai na fad’a maka bai dameni ba in zaka auro dubu ma ni koh a kwalar rigata..
Ido ya sa mata yana kallo ganin ta matso gabanshi tare da tasashi gaba wai sai yaci kamar wani d’anta.
Dariya ma abin ya bashi,a jininta yake,kila ita nata salon nadamar daban yake da na sauran mutane.
Laptop din ta d’auke daga durkushen tare da had’e rai ta kara turo mishi plate tana chunno baki.
Hannu biyu yasa ya riko ha6arshi yana dubenta,bai ga irin Deeja ba har yau, karshe bai san ya sa hannu ba jin zata sau mishi kukan 6aci.
Ruwa ta d’akko had’i da cup ganin ya kusa ya cinye ta durkusa gwiwa biyu tana tsiyaya mishi.
Jarkar take rufe wa lokacin da ya d’auka ya kai bak’inshi zai sha waya tai ringing.
Gaba d’aya su ka bita da kallo na wani dan lokaci, kan cikin zafin nama ta kaima wayar raruma ganin sunan da ya baiyana jiki da sauri ya rigata ya d’auke yana hararata.
Huci take tamkar kububuwa,cike da neman magana ya kara wayar a kunne,dan haka da sauri ta dangwarar da jarkar tare da nufar d’aki tana ta6e baki halamun zata sau kuka.
Gado ta fad’a tare da sakar kuka tana tatta6e baki ba koh hawaye.
Anya zata iya wannan wulakanci kuwa? Jikinta har tsuma yake ganin sunan “SAHIBATA” a jikin screen,bata ta6a cin karo da tsinanniya irin Muneera ba,naci tamkar bakar mayya,gashi zata sa plan nata ya rushe.
Shi kwa yana d’auka ya sau dariya.
“Kai ban ta6a ganin mai daru irin na kawar ki ba sam,she’s very stubborn,yanzun ma riga ta nayi da tuni ta sake fasan waya.
‘Yar dariya itama tai daga chan bangaren.
Iska ya furzar tare da sakar ajiyar zuciya tare da fad’in
“Hoho,Deeja dorling, Allah ya nuna min ranar da zamu tashi bata chakali fad’a ba,ga tsoro yadda ki ka san farar kura…
Zancen shi kawai yake tana yak’e cikin waya,amma chan a kasan ranta wani kishin Deeja ke ratso mata a yau dinnan.
Dan haka firar yau tuni ta gundureta jin duk kusan labarin na Deeja ne,komai ya ce Deeja,dan haka sai ta hau hammar karfi da yaji wanda yasa yai mata sallama.
Ya dan jima dan so yake ya kunnota da tabbatar da ina ta dosa,in ta shirya sauya hali ta nan zai gane.
D’akin ya tura har ta kashe fitila ta kwanta,sai dai yana kunna fitila ta mike ta zauna tare aika mishi kallon tuhuma.
Komai ya ajiye tare da kok’arin hayo wa gadon ta ya ye bargon ta mike durkushe a gadon da kayan bacci.
“Ka fad’a min da mey Muneera ta fini da har ka mato haka a kanta?
Da wani yanayi yake kallonta ganin yadda ta rike k’ugu kayan sun lafe jikinta,matuka sun tafi dashi har yaso kasa controlln kanshi yana had’iyar yawu,chan dai ya cije tare da had’e rai ya d’auke kai.
“Bana ciki da neman fitina ki banni nai bacci dan nasan kin san amsar ba sai an fad’i ba.
Baki ta saka ganin ya kule bargo ya batta,
“Kana nufin kenan ta fini?
Kai ya jijjiga daga cikin bargon,kamin ya nufa kawai ta sau mishi kuka harda su bige-bigen katifa da shura k’afa.
Bargon ya yaye yana dubenta,yadda kasan goyon kaka haka Deeja take wajen 6aci,bai gajiya wa da kallonta,ga nan bakin nan a d’ane tana mishi kunkuni ido ba koh hawaye.
Kai ya jijjiga.
“Toh naji,mey ki ke so na ce yanzu?
Ba musu ta ce
“Ka ce na fita kawai..
Ido ya sa mata,dan tai mishi shiru ya ce
“Toh kin fi..
Kukan ta bari,kan tai magana ya ce
“Amma fa iya tsiwa ki ka fita..
Ido ta sa mishi,dan haka yana kunshe dariya ya miko mata hannu halamun tazo.
Kan ya nufa har ta kaiwa hannun hak’ori ta cije dan takaici,da sauri ya zame yana yarfewa tare da fad’in
“Kai..kai..kai,ki ka cizan?
Da sauri ra ce
“Eh din..
Raruma d’aya yai mata ya chafkota,dama kiris yake jira,dan haka ya hau wayencewa da sai ya rama,daga nan kid’an ya sauya.
#Team Deeja👎🏾 anyi d’an abin kai,da halamun an soma sauya hali,yau 10%✅
SAFHA ne…✍🏾
[4/4, 6:52 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
22_Monday take yau,zo ka ga wai yau su Deeja ne da tashi sassafe d’aura ma miji breakfast.
Yaso makara, dan haka a gurgguje ya fad’a waka ya fuce kitchen dan wai koh dan kwai ya soya da tea.
Kamshi ne ya fara bugarshi tun kamin ya isa kitchen din,dan haka da sand’a ya leka.
Tsaye take tana soya doya da kwai halamun kamshin source ke tashi.
Ciki ya karasa jin tana rera ‘yar wakar
_’A gonata nayi shukar dashe na so bazan cire ba,dole in bata kulawa domin baza naso ta mace ba.. Hmm,umm, hmm’.._
A cikin make murya ,ga nan earpiece a kunne.
Cikin sand’a ya lalla6a tare yi mata dabaibayi ta baya kanshi bisa kafad’arta.
Ihu ta maka da sauri tare da sakar chokalin hannun.
Cika ta yai tare da ja baya ganin ta juyo a dole ya tsoratar ta.
Harara ya d’an sau mata, dan haka da sauri ta chunno baki gaba had’i da cire earpiece din a kunne.
“Har ka tsorata ni..
Doyar d’aya ya ra6a yana juya wa.
“Da ke tsoron bai da wuya ba..
Shiru tai tare da kok’arin kashe wayar,kan ya nufa ta ce
”Ina kwana..
Juyo wa yai had’i da kallonta baki sake.
Iya tsawon watannin da sukai a cikin gidan nan koh da tuntu6en harshe bai jin Deeja ta ta6a yi mishi ina kwana,ya kuma fara tsorata da lamarinta a yanzu ba mamaki ba.
Dan haka kai ya kad’a mata tare da ra6awa ya fuce,tunanin shi d’aya, ace ya fasa auren Muneera yai imani daga ranar Deeja zata dawo mishi gidan jiya,dan wannan ladabin da ta tsiro yafi daukanshi a matsayin toshiyar baki ba wai gaske ba.
Dan haka sai jikinshi yai sanyi,hakan yasa har ya tafi office da ido kawai yake kallonta,duk da bakin nan yana nan d’ane a gaba kamar na gado amma a yau har takalmin da zai sa aka goge mishi,bai son ya saki jiki da yaudarar nan ta Deeja,dan haka dole ya iya takunshi dan sanin inda ta dosa.
Har bakin kofa ta raka shi tana a dawo lafiya,kai kawai ya kad’a mata, har zai fita ta ce zata gidan Maman Ihsan.
Jim yai kad’an, kan daga bisani ya jijjiga mata kai halamun sai ta dawo.
***
“Naji dad’i da har ki ka gane kurenki, amma ya dace ki bashi hak’uri domin wanke laifin ki na baya,a hankali sauran aiyukan ki zai sa ya gane kinyi nadama.
Dabaru ta sake bata,wanda sosai ta san wasu,taurin kai ne ke hanata yi.
Sai bayan azahar ya shigo fuska sake tai mishi sannu da zuwa,shi dai nashi ido,dan haka da kai ya amsa bai da walwala.
“Tare muke da bako,bari zan shigo dashi ki sako hijab..
Bai jira amsar ta ba ya koma waje,ya sani in har ya sanarta da wa suke tare yanzu zai ga sauyi,dan tun ba yau ba in taso ta bakanta ranshi koh a da kamin auren su toh ta kushe halin Abban shi(mai auri saki),dan haka ma yasha mur yanzu,dan yasan ta ganshi sai ta tofa.
“Bissmillah Abba..
Fuska sake su ka shigo da Abban nashi.
Zai nufi d’aki sai ga ta nan ta fito a kitchen sanye da hijab,ja tai ta tsaya tana duben Abban da ke mata murmushi.
Kallota Kamal din ya yi,sai dai da mamakinshi yaga ta sau fuska harda duk’ar da kai na kunya tana fad’in
“Sannu da zuwa Abba..
Da kallo ya bita ganin ta juya kitchen din,da faranti ta fito d’auke da lemon kwali da ruwa da cup tana murmushi,shi dai sai binta yake da kallo.
A gabanshi ta ajiye tare da zama cike da ladabi tana gaidashi,harda tambayar su Badiyya.
Lalle abin kai,wai fitsari da kumfa su Deeja.
Abinci ta koma ta zubo mishi,shi kanshi ya yi mamakin Deeja,dan in yazo rai take had’e wa koh a gida dakyar take magana sai dai ace mishi ai miskila ce Deejan.
Yaji dad’i da d’anshi yai dacen macen kwarai, Insha-Allah yasan zaman zai d’aure.
Koh minti goma bai ba ya ce ai zai tafi a bisa hanya yake,tunda ya wuni ya sake wuni.
Tayi-tayi ma koh abincin bai ci ba,su Deeja harda tsarabar su powder da sarka da gyale wai a kai ma Badiyya.
Da yunwa ya shigo cike da kuma farin cikin tar6ar da Deeja tai ma mahaifinshi,ya sani da uba,uba ne,komai kuwa mugun halin shi,dan haka a yau kad’ai Deeja ta kuma kima a idonshi,dan ta martaba mahaifinshi.
Sai dai yana shigo wa yaga ta rike k’ugu rai had’e sanda zuciyan shi ta tsinke, yasan kenan akwai magana.
Da ido yake kallonta,dan haka sai ta ce
“Wato har Abba yazo garin nan ya kwana ya yini, ya sake yini amma baka sanar ni ba?
Yawu ya had’iye tare da sakar ajiyar zuciya ya ce
“Thank God”
A zuciyarshi.
“Toh daga ina ka ke kai mishi abinci kenan?
Da ido ta tsare shi,dan haka sai ya samu waje ya zauna tare da fad’in
“Gidan Mamy..
Baki ta chunno,har ga Allah bataji dad’i ba,a ganinta ita ya dace ta kai mishi abinci,amma saboda bata isa ba shine bai ma sanarta yazo garin ba.
Hijab ta cire tare da yin d’aki ita a dole yai mata laifi.
Da kallo ya bita tare da jijjiga kai,gaba d’aya ta sauya,sauyi ma na ban mamaki.
Abinci ya janyo tare da daukan chokali yana sake kallon d’akin da ta shige, yasan fushi tai a dole,shi kam mutunci ya kare bai san zai samu hakan ba,dan haka sai yai murmushi tare da kai abinci baki.
Deeja kam she’s impossible a gareshi.
SAFHA..✍🏾
[4/4, 6:52 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
23_D’akin ya shiga bayan ya gama cin abinci ya hau rage kayan jikinshi ya d’an kallota ganin yadda ta turo baki kai gefe.
Ba sai ta fad’a ba,halin da ta nuna zai gane fushi take,har da su juyar da kai halamun baza ma ta kalleshi ba.
Kai ya girgiza, in Allah ya gama ka da rigimammiya ai sai godiya kawai.
Dan haka iska ya furzar tare da zama bakin gadon.
“Naji ban kyauta ba,a gaba zan sanar ki,shikenan?
Juyo wa tai tai tare da sakar fuska ta kad’a kai.
“Zan huta ki tada ni in an kira sallah, and ki shirya zamu wani guri anjima da yamma.
Kai ta sake kad’awa tare da gyara mishi ya kwanta duk da bai fi
Kamar mai gadi haka ta sashi a gaba tana dan satar kallonshi ganin yai bacci.
Tsam tai,taurin kai yasa ta kasa kare ma Kamal din nata kallo,tabbas ya yi ne,yai mata karshe,duk da mutum tara yake bai cika goma ba amma a gunta Kamal ya cike,a baiyana ne dai an tsaya taurin kai da jan aji..
Ke ki ka sani,bari Muneera ta shigo
#Tean Deeja 💃🏾.
Ido ya bud’e a hankali tare da kannewa ta yadda ba zata gani ba jin an fara kiran sallah, sai hannu ta ke kaiwa amma ta rasa ina ma zata ta6a.
Hannu ta mika kan pillown da zummar ta buga duk yana kyallota.
Ido ta zaro jin an chafki hannun kam,dan haka sai ta kafe mishi da ido.
Kanshi ya d’aura bisa hannun yana murmushi, dan haka sai ta dan duk’o jin matsewar hannun tana dubenshi.
Ido rufe ya ce
“Gadin mijinki ki ke hala?
Baki ta turo gaba tare da dan 6ata fuska kamar gaske.
“Gadi kuma?
Kai tai saurin girgiza wa halamun ba a’a.
Ido ya zuba mata jin tana gunguni baki a d’ane,kai ya girgiza.
Ya riga da ya zama jinin jikinta wannan turo bakin,dan haka bata nufa ba ya dan make bakin da yatsunshi tare da sauka ya shige band’aki ya batta da gunaguni rike da baki.
****
Gida ne dai-dai misali dan duf dashi mai upstair ya kawo ta.
Ba wani babba bane,dan tsakar gidan bai da fad’i, amma sosai tsarin ginin yai mata,dan matuka tana son gida mai bene marar fad’i dad’in shara.
Kallota ya yi,kamar yadda take kallonshi da halamun ina ya kawo ta?
Murmushi ya yi tare da miko mata hannu halamun ta sako nata.
Hannun ta kalla,kamar ba zata sa ba sai dai ta mika mishi ya had’e su gu d’aya tare da fad’in su shiga.
Ba musu ta bishi hannun su sakale da na juna.
Ba wata karya a gidan na tarikice,sai dai an gama komai har fenti da su sa tiles,matuka ya tsaru asiri a rufe.
Ba komai cikin parlourn sai labule da dispenser da a.c standard.
“Gidan ki ne…
Juyo wa tai da sauri jin ya rad’a mata,cike da murna ta wangale baki harda dan tsallenta ta nufi d’akin dake kallonta.
Shima labule ne kawai a ciki sai bathroom.
Shima d’ayan, sai dai d’aya yafi d’aya girma.
“Kai,amma yai masifar tsaruwa, muje sama toh..
Da kallo kawai yake binta ganin yadda take murnar, da yasan za tai murna haka ai da tun tuni ya kawota.
Binta saman ya yi ganin ta haye da dan gudunta cikin murna,sai ya girgiza kai.
Ciki ne shima da parlour sai bathroom kawai,labulen ta zuge tare da shakar iskar da ta buso tana lumshe ido.
Komai tamkar ya tambayeta,bata ra’ayin tafkeken gida da wasu alatu,tafi bukatar rayuwar sauki in dai akwai soyayya.
Dan haka hannu ta hau yarfe wa cikin murna har bata san ma ta riko hannunshi ba.
“Tamkar ka shiga cikin raina Allah yai min kyau sosai.
Murmushi ya yi had’i da girgiza kai, kenan yanzu ta shirya zama dashi?
Ido ya sa mata tamkar mai son karantar zuciyarta,jin ya yi shiru sai ita kawai ke zuba yasa ta kalloshi.
“It means kin shirya zama dani kin ajiye Burin naki gefe?
Kai ta saukar,mey za ta mishi ya gane duk abinda ya faru ya wuce,ta zubda makamen yakinta ta hak’ura?
Bata sani ba,dan haka jin tayi shiru yasa ya zame hannunshi da ta rike.
“Ki zabi wanda ki ke so,sama koh kasa,Insha-Allah tare da amarya zamu tare..
Da sauri ta kalloshi tare da yin kicin-kicin da fuska tana sau mishi harara.
Ganin haka yasa ya sauko kasa,yana jiyota tana fashewa da kuka mai sauti ba koh hawaye.
Da sauri ta d’auro a bayanshi tana fad’in
“Wallahi bata isa ba,ai gidana ka ce, dan haka ba abinda ya dameni da wata amaryar ka ni kad’ai ce mamallakiyar cikin gidan nan ba wajen zaman wata ‘yar katuwa..
Ja yai ya tsaya tare da juyo wa bayan ya gama sauka had’i da hard’e hannu a kirji.
“Gidan ki koh nawa?
Cikin sauri ta karaso tare da fad’in
“Nawa.. Dan yanzu ka gama fad’a a nan wajen zai iya mana sheda..
Wajen da suka tsaya dazun take nuna mishi ya kalla,dan haka sai ya hau girgiza kai tare da fad’in
“Toh su6utar baki ne,amma ni ne mai gida,ni kuma ke da iko da gida in sarrafashi yadda nake so..
Ido ta sa mishi ba koh kiftawa, kamin ya gama bayanin nashi ta sau mishi bori akan afafur ba fa zata yadda ba.
Karshe da rigima aka dawo gida tana ta mishi bori had’i da kuka ba hawaye,kai ya jijjiga, yasan nata wasa ne,amma zai nuna mata shi kam aure ba fashi,dan baiga halamun ta damu dashi ba,da kishiya kawai ta damu.
SAFHA ne…✍🏾
#Team Deeja get ready🤣🤳🏾.
[4/4, 6:52 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
SADY JEGAL.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
24_Da safe yana fita gurin aiki ta figi hijab d’inta sai gidan Maman Ihsan, da shigarta kuka ta sau mata tamkar wata k’aramar yarinya.
Sai da ta kimtsa Ihsan sannan ta zo ta zauna tana kallonta tana sauke ajiyar zuciya.
“Yau kuma wace rigima aka d’auko? Saboda nasan keda mutumen kun koma tamkar wasu Tom da Jerry, bansan iya lokacin da matsalarku zata zo k’arshe ba..
Ido ta matso duk da hawayen ya kafe.
“Ke fa ki ka ce na sauke komai na kyautata mashi duk wani abu zai wuce, kuma gashi nayi d’in,amma sai wani kalar cin fuska ke k’ara kunno kai.
Ajiyar zuciya Maman Ihsan din tayi tare da girgiza kai.
“Deeja laifinki ne koma meye, amma nasan Kamal bashi da matsala dai-dai gwargwado, amma duk da hakan gaya min mey ya faru?
Zama ta gyara tare zum6oro baki.
“Duk fa abinda kika ce har wanda baki ce ba ina k’ok’arin yi mashi,shine fa jiya ya ce in shirya zamu je unguwa, nan ya kaini gidan da ya gama gini wai na za6i d’aya,sama koh kasa wai ni da Muneera ne,ji fa dan Allah.
Wani kukan take neman saka tai saurin riko hannunta.
“Kin san mey?
Kai ta girgiza mata,dan haka sai ta cigaba.
“Abu d’aya nake so dake ki kauda kanki akan maganar aurenshi, kici gaba da….
“Haba Maman Ihsan,in fa kauda kaina kika ce? K’awata fa zai auro,koh kin manta?
Baki sake Maman Ihsan din take kallonta,jin batai magana ba yasa ta cigaba.
“Ni bama wannan ba, duka-duka aurenmu wata nawa ace Kamal zai min kishiya? Ki fa duba,wannan ai cin fuska ne da abin fad’e a gari,kowa tambayarshi mey nake mishi? Mey zance?
Numfashi ta sauke tare da furzar da iska,ta ma rasa mey zata ce,dan haka sai Deejan ta cigaba.
“Haka fa naci borin kukana amma yana sa min ido,wallahi toh gab nake da na tafka mishi tsiya..
Ido da sauri Maman Ihsan ta waro,harara ta sau mata tare da fad’in
“To shikenan ki sauke komai kiga hakan zai hana shigowar kishiyar inda muga.
“Ina fa son ki gane cewa shure-shure baya hana mutuwa, amma kyautatawar zai ja maki wata martaba a idonshi koda kuwa bai nuna maki hakan ba,kije ma kila gwada hankalin ki yake da kinyi kuskure d’aya zai gane naki wasa ne..
“Sannan ina son kigane cewa Kamal bazai iya gane cewa sauyawarki ta har abada bace har sai kin jure da hawa hanyar da kika dosa, kuma kinsan da bakinki kika furtan cewa yana maki kallon tamkar duk abinda kike yi don ya fasa aure ne koh?
Jim tai tana nazarin zancen,dan haka sai ta daga mata kai halamun hakane.
“Amma ke a naki tunanin me kike gani a zuwan mafita yanzun?
Zama Maman Ihsan din ta gyara ganin ta sakko da ita,
“Yauwa,haka nake son ji..
“Mafita d’aya ce ki k’ara kulawa dashi sama da yadda kike yi a da, kuma ki ajiye maganar Muneerat a gefe, a kullum ana so Mace ko su hud’u suke gun miji to kowacce ta sakawa ranta tamkar ita kad’aice a gidan, da hakan zaki samu nutsuwar kulawa da mijinki..
Jim tai tana tunani,anya zuciyarta zata iya nutsuwa in ba taga karshen scene din nan ba?
Kishi ne,ta sani kishi ke matukar damunta, dan da kyar ya bari ta iya bacci.
Ajiyar zuciya tai tare da fad’in
“Toh,Insha-Allah.
Hakan ta yiwa Maman Ihsan godiya ta koma gida.
****
Sosai ta dane kishi ta rika ta cigaba da bawa Kamal kulawa kamar yadda Maman Ihsan ta ce.
Yau kawai taji tana sha’awar yi masu d’anwake da garin da Maman Ihsan ta basu, hakan ta zage damtse tayi d’an waken da yaji kayan yaji sannan ta shiga toilet ta tsalo wanka.
Gaban dressing mirror taje tayi kwalliyarta dai-dai misali ta dawo falon ta zauna tana zabga wani uban k’amshi.
Haka kawai take jin wani nishad’i cikin ranta.
Murmushi tai tare da kallon agogo,tasan gab yake da zuwa,a yau ta shirya nuna ma mijinta tar6a ta ban mamaki,a yau Insha-Allah zata nuna mishi ita Deeja ta banbanta da saura,bata bukatar rigima a yau sai nishad’i da tsantsar kulawa.
Dan haka take ta Allah-Allah ya dawo tai ar’ba da Kamalunta,duk da bazata ce abin so bane,amma tabbas tasan a shirye take da ta kare rayuwarta tare da Kamal.
Kai ta jijjiga cikin lumshe ido lokacin da ta tuno iya salo na Kamal.
A karo na uku kenan tana kaiwa agogo kallo had’e da sake kiran wayar amma bata shiga.
Baki ta chunno gaba tana mai nazarin mey ya tsaida shi har 03:00pm?
Mike wa tai jin an bud’e kofar gidan had’i da taku.
Rai ta dan had’e tare da sake d’ano bakin gaba halamun tai fushi.
Sai dai ganin wacce ta bud’e labulen ne yasa ta gyara tsayuwa tare da had’e girar sama da ta kasa.
“Assalam Alaikum…
K’ugu ta kama tare da mata kallon sama da kasa cike da baki isa ba.
“Babu aminci a tare da ke,dan haka bazan amsa ba..
Kofa ta nuna mata da yatsa.
“Tun muna iya shaida juna dake ki fuce min a gida dama..
Murmushi ta dan yi lokacin da ta kare mata kallo,tabbas a da bata zata za m ta iya had’a ido da Deeja ba dan kunya,amma a yanzu dai-dai take da ta fuskanci zahiri,dan haka cike da kishi take kallonta itama.
“Dama ba zama nima nazo yi ba,magana nazo…
“Ki fuce na ce,munafuka bakar algunguma,wallahi kinyi asara,ke kinsan nafi karfin na had’a miji dake,wannan sai dai cikin mafarki..
Rai ta had’e
“Gaskiya kar ki kara ce min munafuka…
“An fad’a munafuka, maci amana,wacce tai kwantai babu mashinshini kawai..
Ido Muneeran ta rintse da sauri jin maganar kamar dirar mikiya, sai dai dama ta kwan da sabon Deeja ba kyal ba ce.
A zabure ta nufi kitchen ganin zata tsaya 6ata mata lokaci ta hau dube.
Kan wata duk’urk’urar ta6aryarta idonta ya kai,dan haka cikin zafin nama ta sungumeta fatanta shine ta riski Muneera yau zata ga karshen iskanci.
Jaye yake da akwatuna seti shida tare da wasu almajirai uku duk sun taya shi d’auka.
Da tsabar farin ciki ya iso,sai dai jin ihu yasa da hanzari ya karasa.
Tsere ake tsakanin Deeja da Muneera wai a dole sai dai ta tsaya ta kwad’a mata,dan haka su ka fara kewaye round na kujerun parlourn Muneera na ihun a taimake ta.
“Shegiya bakar algunguma kadan ba sai kin tsaya ba,yau zan nuna miki karshen iskanci,ba mijina ki ke so ba?…
“Subhanallah…
Duk juyawa sukai bakin kofar jin maganar..
“Kanki d’aya kuwa?
Kai tai saurin girgiza wa tare da fad’in
“A’a, dubu ne,amma yau sai dai a ni koh ita..
Da gudu ta sake yin kan Muneeran da ta6arya yai hanzarin isa,kan ta farga ya shige gaban Muneeran ya kare mata.
Ido ta k’ank’ance da zummar surfa bala’i su ka ji ana fad’in
“Ina zamu ajiye akwatinan?
Da sauri ya warce ta6aryar lokacin da ya ce
“Ku shigo dasu ciki..
Yana hararar Deejan.
Mutuwar tsaye tayi baki sake daga ita har Muneeran su na bin akwatinan da kallo wanda almajiran ke sauke wa.
Kamal din ta kallo tare da nuna akwatinan da hannu bakinta na ka’rkarwa ta ma rasa mey zata furta.
“Eh kayan aure ne,na fad’ar kishiya,ki ma ji da wai,abu har ina murna ya fara saituwa ashe kina nan da…
Shiru ya yi ganin hawaye na ziraro mata ta kuma kafe akwatuna da ido.
Kai ta dago da zummar mishi magana taji wani abu ya tokare makoshinta.
“Muneera zo ki wuce,sannan ki sani aure kam ba…
Luuu tai baya da halamun fad’uwa tana rike da kai da azama ya taro ta wanda hakan ya hana ya k’arasa maganarshi.
“Innalillahi… Deeja!!!!
Jijjiga kafad’unta yake ganin jikinta ya sake ga nan hawaye na tsiyaya wanda su ka makale a idonta,Deeja kam da halamun an sume.
#Team Deeja kuyo agaji da ruwa k’ank’ara kar ta lula, dan aure ba fashi😜
SAFHA…..✍🏻
[4/4, 6:52 AM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©SAFHA.
25-“lnnalillahi…..”
Jijjiga kafad’unta ya kuma yi tare da kiran sunanta duk ya kid’ime ya rud’e ya rasa Abinyi sunan ta kawai yake ambata, “Deeja!!!
Ganin rud’ewar da Kamal yayi yasa Muneera tayi hanzarin d’auko gorar ruwan dake saman center table, bai bari ta bud’e ba ya amsa cikin hanzari ya bud’e ya shiga yayyafa mata ruwan a hankali yana shafe mata fuskar da ruwan cike da tausayawa.
Ganin hakan yasa Muneera ta nufi k’ofa ta sallami Almajiran da sukai tsaye carko- carko suna ganin ikon Allah.
Ganin Kamal rungume da Deeja hankali tashe gashi har zuwa yanzun bata farfad’o ba ya sata d’aukar gorar ruwan ta shek’awa Deeja a fuska take taja dogon numfashi ta sauke,
A hankali ta bud’e idanuwanta wanda ke lumshe,
Saida ta bude idon tangargar ta shiga binsu da kallo d’aya bayan d’aya,
take Abun da ya faru ya shiga dawo mata d’aya bayan d’aya, a k’arshe ta sauke idonta akan akwatinan da Kamal ya kira da natane na fad’ar kishiya.
Nan ta daddage ta d’ora hannu aka ta kurma uban ihu tare da sassank’amewa tamkar wacce zata tada Aljanu.
Shure-shure take tana wani sassank’amewa tana kurma uban ihu tana ture Kamal wanda yake k’ok’arin rik’eta yana ambatar sunan ta.
Amma ina harbe- harben da take ya hana shi kamota duk tabi ta rud’ashi ya rasa ta inda zai kamota, daya ruk’ota tanan ta zille ya kuma ruk’ota ga sambatun data shiga zayyano masa kusan ma shiyafi d’aga hankalin sa.
Duk wannan dramar da suke Muneera na gefe tana kallonsu cikin k’unshe dariya don tasan wannan yana d’aya daga cikin tab’ara irin ta khadeeja inhar tana son Abu to babu kalar rigimar da baza tai ba a kansa.
Don haka cikin sanyin murya da nuna Alamun jimami ta karya wuya ta shiga fad’in,
“Sannu Deeja. Kamal ni fa gani nake kamar Aljanu ne da Deeja kaga fa abinda take mai Aljanu zam”.
Kashe masa idon da tayi ne yasa ya gano zolaya ce take kuma yagano bakin zaren don haka ya k’unshe dariya,
“Kinsan kuwa nayi zargin Aljanun gareta don naga haka masu aljanun suke suita fizge- fizge sai an musu ruk’iyya suke denawa”.
Jin hakan yayi matuk’ar kad’a cikin Deeja don ita a duniyar nan babu abinda tafijin tsoro irin Aljani, duk da ta tsorata dajin ya ambaci ruk’iyya bata fasa sassank’ame wa tana haure-haure ba.
“Kasan kuwa Malam Audu na bayan layinmu yana ruk’iyya har zane aljanu yake inba dama kawai mu kaita can”.
Dariya yake mata k’asa-k’asa don ganin ta kasa kunne ta gama nad’e abinda suka fad’a, suna kaiwa aya kuma ta d’ora daga inda ta tsaya.
“Ai kawai ruk’iyyar zamu kaita don wannan Abu na Deeja bafa na lafiya bane”.
Jin da gaske anfara taga-tagar d’aukar ta za a kaita gun ruk’iyyar ya sata daddage k’arfinta ta hankad’a Muneera ta gwarata da bango jikak’e k’um! K’eyar ta tabada sauti.
Shikuwa Kamal tureshi take amma ta kasa kwacewa saida ta daidaici dantsensa ta gasa masa cizo aekwa babu shiri ya saketa tai baya tana huci.
“Saidai kiga Aljanu akanki bak’ar munafuka algunguma maciya amana butulu kawai” ta fashe da kuka.
” kuma ni saina nuna miki k’arshen rashin mutunci ba dai ni Deeja kika ciwa Amana ba sannan kika tako kika zomin har gida? To yau sainai miki Abinda zaki nadamar cin Amanar da kikai min”.
Tajuyo kansa “kai kuma tunda kaga wannan matakin daka d’auka to shine dai-dai a gurinka to nima zan d’auki nawa matakin”.
A fusace ta fuce daga falon suka bita da ido duk sun tsorata da ganin yanda ta birkice musu Ashe darun Deeja na baya wasa ne? Yau dai sunga b’acin ranta, Adalilin me? Kishi, kishin Kamal?
Tabbas amsar haka yake.Cikin rawar murya Muneera tace’ “yaya Kamal ni fa na tsorata da Deeja ka bita kar muje wani Abu yafaru azo ana nadama agarin neman k’iba a samo rama”.
Baiko tankata ba yabi bayan Deeja don shima ya tsorata da ganin yanda ta fusata duk wani karsashi nasa ya k’are, tausayinta shike lugude cikin ransa, yasan duk abinda takeyi donshi takeyi kishinsa take nunawa k’iri-k’iri don tak’i yarda da hakanne.
A bakin k’ofar falon sukai kacib’us, gabansa ya yanke ya fad’i don ganin hannunta d’auke da jarkar kananzir ga ashana a d’ayan hannun.
Cikin karsashi yayi kanta ta dakatar a tsawace, ” karka kuskura kayi yunk’urin hanani kana k’arasowa ina shek’a maka kuma babu abinda zai hanani kyatta ashana gwara na kashe ka nima na kashe kaina kona huta da wannan azababbiyar rayuwar da nake ciki”.
“Dan Allah kar kiyi Deeja tsaya ki saurareni kar kiyi abinda zaki yi nadama a gaba”.
Hannu Muneera ta d’ora aka tana kiran sunan Allah idon ta a waje tamkar ya fad’o k’asa don tsoro, ” tsaya Deeja karki k’onamu tsaya kiji gaskiyar lamari wallahi ni ba aure miki miji zanyi ba kitsaya nai miki bayanin komai karkisa mu shiga uku wayyo Allah na”.
Wani mugun kallon rainin hankali Deeja ta watsa mata mai fassarar, k’aryar ki tasha k’arya Muneera.
Cikin zafin nama yayi kanta da nufin ya murd’eta ya k’wace, kan ya k’arasa gareta ta daka tsalle tayi gefe bai samu damar rik’eta ba.
Cikin hanzari ta shiga kici-kicin bud’e jarkar Muneera ihu take tana fad’in ” wayyo mun shiga uku Deeja kitsaya kiji karki bud’e jarkar nan”.
Cikin zafin nama yayi kanta saidai kan ya k’arasa ta bud’e ta fara tuttulawa akwatunan yana zuwa daf da ita ya daki jarkar tayi gefe tana d’agowa ya wanke ta da kyawawan mari har sau biyu.
Cikin wani irin yanayin daya fad’ar masa da gaba ta d’ago dafe da kunci, zazzafar k’wallar data dinga rige-rigen sauka kan kuncinta ita tafi kashe kuzarinsa yasan lallai yau yayi laifi ga Deeja don duk rigimar Khadeeja bata kuka mai hawaye sai dai tagama bige-bigenta da zunb’ure-zunb’ure da k’unkuni.
Cikin rawar murya da rawar baki duk jikinta rawa yake ga hawaye shab’e-shab’e “bantab’a dana sani ba irinta yau tunda na tsinki kaina cikin rayuwarka, haka za nayi alkawaririka na k’arya duk a dalilinka, to kasani yau ce rana ta k’arshe da zaka k’ara tozali da k’wayar idona, zan barka kayi rayuwa da Muneera don zuwa yanzu nagane ta taka matsayin da nayi kad’an ni nasameshi a gurinka tunda gashi kad’au hannu ka mare ni sabida ita”.
Ta juya gun Muneera, “ki zuba ruwa a k’asa kisha kinyi nasarar rabani da duniyar ma baki d’aya ba Kamal kad’ai ba, inhar nacika y’ar halak nabarku har gaba da Abada”.
Da gudu ta kwasa tayi d’aki da gudu ta mayar da k’ofa ta rufe ta murza key.
Hawaye keson zubo masa yana cijeshi da dauriyarsa amma sai da guda d’aya ya d’uso kan kumatunsa, cikin k’araji Muneera ta shiga yimasa magana da cewa’ “Meyasa kayi haka Kamal?”.
“In banyi hakan ba so kike na k’yaleta ta halakamu?”.
“To ni dai zanje na fad’awa Deeja gaskiyar Abinda yake faruwa zuwa yanzu yaci ace tasan komai ko nafuta daga zargi tadena tsinemini daga Abin arziki”.
K’arar da sukaji ta kwallane yasa suka nifu k’ofar da gudu har yana ture Muneera ta fad’i akan hannun ta takwa saka k’ara ta rik’e hanun.
Kamal kuwa bai ma san abinda yayi ba hankalinsa yayi gaba ya tsorata da k’arar Deejansa.
Itama daurewa tayi ta mik’e ta isa k’ofar d’akin suka shiga bugu tareda kiran sunan ta.
” Kiyi hak’uri ki bud’e Deeja kar kiwa kanki illah in har akan maganar aure ne na fasa bazanyi ba ki bud’e kofar kiji nayi Alk’awarin dake k’adai zan rayu, matsayinki na nan yanda yake ada, nai miki rantsuwa da Allah har yanzu ina sonki banida tamkarki ni Kamal naki ne ke kad’ai ki bud’e dan Allah”, bubbuga k’ofar suke amma shuru kakeji wai malam yaci shurwa.
Kuka sosai Muneera take, ta mafi Kamal tsorata da lamuran Deeja don duk inda akaje aka dawo itace a cikin rikici itace zata shiga uku daga abin Arziki ya zama na tashin hankali.
Don haka batasan sanda tasoma warware k’ullin ba.
“Wayyo Deeja ki saurareni wallahi ba da gaske auren Kamal zanyi ba niba maciya Amana bace bazan tab’ai miki butulci ba, babu komai tsakanina da kamal sai plan wanda shida kansa ya shirya hakan, ni kuma na amince sabida dalilan daya kawo min, amma wallahi ba aurensa zanyi ba bazan tab’ai miki wannan cin Amanar ba ko wata naga zatai miki sai inda k’arfi Na ya k’are”.
Surutai maganganu rantsuwa babu kalar wacce basu yi ba amma shuru, wannan ya kuma d’aga hankalinsu, suka k’ara k’aimi wajen bubbuga k’ofar ko zata bud’e nan ma shuru.
Saida suka gama jigata sannan ya tuna da safayar muk’ullan don haka ya nufi d’ayan d’akin da gudu don d’auko muk’ullan.
#Team Deeja yau ranar takuce😜
SAFHA……✍🏼
[4/4, 8:12 PM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
©SAFHA
26-Tana murza key d’in tazare tayi wulli dashi ta kifa kan gado ta k’udundune cikin bargo zuciyarta nai mata d’aci yayin da ta shiga kukan zuci hawayen ma ta nemeshi ta rasa.
Dafe k’irjin ta tayi don wani irin nauyi taji zuciyarta tayi ta kasa banbance meke damun zuciyarta, k’uncin dake dank’are cikin ranta shiya tokare mak’oshinta tagagari ko shak’ar iskar kirki.
Ganin tana neman hallaka kanta yasa ta yunk’ura ta tashi hannunta dafe da k’irjinta, tana k’ok’arin ziro da k’afafunta ta soma jiyo sautin maganganunsu,
Nan ta kuma kasa kunne don taji abinda suke fad’a rad’au kuwa tana jiyosu.
Mamakin jin furucin sune ya mantar da ita halin da zuciyarta ke ciki sai ma ta kinkimo tunanin rainin hankaline suke son yimata, yama za’ayi su canja magana bayan tana sane da hatta manya sun shiga cikin maganar ko gidan daya gina yayi shine sabida ita da Muneera sai yanzu rana tsaka don ta birkice musu sai su nemi raina mata wayo?.
Amma kuma rantsuwar da taji sunayi bilhakki babu batun wasa a cikin ta bare ma intai la’akari da yanda Muneera ke zayyano Abinda ya faru wanda zuciyarta ta kasa k’aryata Muneera don tasan Muneera bata k’arya kuma ko cikin wasa ne baza tai maka rantsuwa akan k’arya ba.
Jinsu kawai take ta rasa me ya kamata tayi sai canki-canki take tsakanin k’arya da gaskiya, take ta yanke shawarar kiran Mamy don tasan Mamy ce ta bashi goyon bayan auren Muneera kuma babu ta yanda za’ayi Mamy taimata wasa.
Bugu d’aya ta d’aga kiran ko sallama babu ta rushe da kuka wiwi, sanin hali irinna da Deeja yasa Mamy bata damu da kukan nata ba, ta tsaya tana sauraran kukan har ta tsagaita ta samu damar magana.
“Yanzu Mamy dasa hannunki Kamal da Muneera suka dinga Kwallo da zuciya ta? Ashe duk maganar aurensu shiri ne Mamy amma baki fad’amin ba? Ni bansan sanda Kamal ya tsige matsayina ba ya kafa kansa gurinki yanzu ko Abba baya sauraro na sai kamal”.
Murmushi Mamy ta saki dama tasan za’arina don tunda Kamal da Muneera suka kawo mata akwatunan kayan da yayi mata tagani a madadin kayan laifenta dabai samu damar yinsa ba a wancen lokacin tasan yau k’wan zai fashe fatan ta dai Deeja tayi karatun ta nutsu tasan ba itace autar mata ba, ba kuma don ya nemi wacce zata soshi yarasa bane yake zaune da ita tana shuka masa rashin mutunci,
Don haka tun d’azu take sauraran kira daga Deeja sai gashi kuma ta kira d’in.
“Kina jina Deeja? nasan komai akan hakan kuma nina bada goyon baya don inaso naga rayuwar d’ana ta inganta, Kamal Namijin duniya ne a yanzu duk duniya baki da tamkar sa, basai nace ki sauke abinda ke kwanyar kanki ba, kinga dai misali yanzu ko? To sati biyu na baki kacal in har kika koma ‘yar gidan jiya ba sai na fad’a miki hukuncin da zan zartar ba, ince dai kina sane da Kamal mijin mace hud’u ne? to Allah ya taimaka”. Tana kaiwa aya ta katse kiran.
Kusan mutuwar zaune tayi don tsananin mamaki bin wayar take da kallo bayan ta sauke ta daga kunnenta cikin sanyin jiki.
Murna za tai ko kuka ko haushin rainin hankalin da sukai mata? Tsam tai da ranta tana tunanin wani abu, So! Tabbas Kamal k’waro ne a wannan fagen, cijewar da take ne ke sagar da karsashinsa, to in kuma ta bada nata gudunmawar kuma fa? Ya abin zai kasance? “Tabbas zaifi armashi”. tabawa kanta amsa a sarari.
Habawa ai batasan sanda ta buga tsalle ba harda k’ara “yes”, nan ta shiga kwaso shoki da itigi duk wata damuwar ta tayaye.
Jin k’arar mukullayen da suke gwadawa yasa tayi sauri tai zaman dab’aro tareda dafe kirji ta shiga hakin k’arya harda kiran wayyo.
Zaman ta yayi dai-dai da bud’ewar k’ofar don haka sukayo kanta cikin hanzari har rige-rigen d’agota suke tare da kiran sunanta duk sun damu mutuk’a.
“Sannu Deeja” da hannu ta dakatar dasu, “Karku kuskura ku tab’ani kubarni na mutu na barmuku duniyar kucita da tsinke”.
Sororo yake bin ta da kallo don ganin ta k’ak’alo damuwar dole tana shimfid’ata kan fuskar sa.
Sosai ta matso kusa da ita ta kamo hannayenta duk da tana fiffizgewa.
“Ki yarda dani k’awata, nisam banci Amanar kiba Deeja kitsaya ki saurareni na rantse miki da Allah babu wata maganar soyayya tsakanina da mijinki balle maganar aure, shi da kansa ya buk’aci mu shirya hakan don kigyara gurb’atattun halayenki, wanda kika k’agawa kanki, amma kisani ni Aminiyar mai k’aunar ki mai son ci gabanki, bazan tab’a bari abu mara dad’i ya same ki ba, wannan dalilin yasa na amince da buk’atar Kamal kuma ban yarda kai tsaye ba saida Mamy tasa baki, kiyi hak’uri Deeja kar kimin wata fassarar daban nayi hakanne domin Allah don kuma na ceto rayuwar aurenki daga lalace wa kuma ina son martabar ki tak’aru gurin mijinki a maimakon ta ragu”.
Cikin harara da murgud’a baki had’i da murmushin daya taso tun daga cikin ranta ya fallasa asirin zuciyarta, ta matso kusa da Muneera sosai suka rungume juna suna murmushi.
Kallonsu kawai yake yana daga gefen hagun ta, suna cika juna ya mik’o mata hannu tareda cewa” saura ni”.
Juyar da kai tayi ta cunno baki, alamun har yanzu bata huce ba.
“Yanzu in banda abinki Deeja inhar naso mijinki yaya zanyi da yaya Salis Wanda baikonsa ke kaina? Zaro ido tai had’a da dafe goshi kana tace’
“Yanzu har da yaya Salis a had’a bakin?” “Kwarai kuwa don yana son kwanciyar hankali gaba d’aya, bari nakira miki shi ya kuma jan wannan kafaffen kunnan naki”, ta d’anja kunnen, “wayyo”.
Ta saki k’ara cikin salon shagwab’a, hakan da tai yayi matuk’ar tasiri agunsa har yaji wasu lamura sun motso masa ya sakar mata murmushi ta kuma kauda kai bakin nan kamar ya tab’o hanci.
Shima yaya Salis fad’a ya k’arai mata harda had’awa da baraza na, karshe dai Muneera ta amshi wayar tayo falo don tabasu guri itama tasamu damar ganawa da masoyin ta.
Hannu ya mik’a mata “zo nan Deeja”, bakin ta kuma turawa gaba harda mak’e kafad’a.
“Kizo kinji Deeja na,
Ina buk’atar batutuwa da dama daga gareki, kisani, yanzu duk wata hayaniya tazo k’arshe tsakanina dake, akwai damar da nake nema a gareki a yanzu, ki tausaya mini ki tausayawa zuk’atanmu ki dena wahalar dasu ki basu abinda suke buk’ata fiye da komai cikin duniyar mu Deeja”.
ta soma ‘yar dariya cike da kunya ta sunk’e fuskarta cikin tafin hannun ta.
Ganin hakan ya k’ara masa k’warin guiwa ya kuma samu tabbacin Deeja na sonshi don haka cikin kuzari irin wanda farin ciki yake haifar wa yace,
“Deeja d’ago idonki ki dubeni”.
Da k’yar ta sarrafa kanta ta d’ago ta dubeshi jikinta na tsuma a sanadin kusancin dake tsakaninsu, k’wayar idonsu ce ta hard’e ya shiga wani matsanancin yanayi ta kwaci idon ta da kyar cikin shauk’in dake tunzura zuciyar ta.
Cikin dabara ya lalubo hannunta ya shiga murzawa “tafuka masu laushi”, murya tausashe yace’
“Kimin Alfarmar so Deeja zumunta tajamin sonki mai k’arfi ya kusanci zuciyata, ina neman raddi don Allah, ki taimakeni Deeja ina neman soyayyarki,
Don Allah karki zauna dani don alfarma”.Yai mata rad’a a kunne,
“So nake naji so a bakinki, so nake ki bayyana min so”.
Ta d’ago da kanta sosai ta kalleshi hawaye na taruwa a idonta murya na rawa.
‘Duk Abinda kake so na zama zan kasance zanyi ba bisa Alfarma ba bisa cancantar ka”.
Jintai shuru, ya gyad’a kai, “ba buk’atuna kenan ba, amsar so nake so bana biyayya ba Deeja ina sonki!”.
Numfashinta taji na neman d’aukewa sabida murna da farin ciki, tace,
“Nima haka”.
Ya yawota jikinsa ya rungume yana jiyo sautin bugawar zuciyarta wanda suke nuni da zallan soyayyar data bak’uncesu.
Cikin sassarfar numfashi yace” kema me? “Ina sonka! Ban tab’ajin son wani abu sama da kaiba, babu wani abu daya tab’a birgeni sama da kai, ni ba zumunta ta rayamin son kaba wayar gari nayi na tsinci kaina cikin son ba tare da nasan dalilin saba……in wannan ne buk’atar ka kayi farin ciki kasamu”
“Mafarki ko gaske?”.
Tana murmushin da bai tab’a ganin mai kyau irin saba, so kenan!
“Dame kakeson na tabbatar maka ba mafarki kake ba?”.
Ya kuma ware hannu, ” zo gare ni”,
Cikin hanzari da b’arin jiki ta kuma shigewa jikin suka k’ank’ame juna tamkar su koma halitta d’aya.
kuka tafara a yayin dataji yanda zuciyarsa ke harbawa, hannu tasa ta dafe k’irjinsa “yaya kamal me yake faruwa da kai?”.
Ya amsa cikin shauk’i” sonki ne Deeja, zuciya na murna da samun Abinda takeso bazan iya dakatar da ita da farin cikin da take nunawa ba, ina sonki Deeja nayi murna da kika yarda kika aminta zaki rayu dani cikin so da aminci”.
Ta kuma b’arkewa da kuka, ” nayi nadama yaya Kamal ka gafarceni don Allah ban san sonka ke sani hauka ba tuntuni bansani ba, ka yarda dani ina sonka”.
Tuni yayi nisa dajin jiki a b’arinda masoya keyi idan suka tsinci kansu cikin na shauk’i, sunsunar ta yake tareda sunbatar ta yana numfarfashi ya rasa ta inda zai nunawa Deeja yanda ya kejin ta don haka ya soma nunawa a aikace…..
“Muneera”, ta ambata tare da janye jikinta tana haki.
“Sai yanzu kika tuna da ita?”.
Yana k’ok’arin mik’ewa tare da cewa’ “bari nadubota saina kaita gida na dawo”.
Nan ya gyara mata rigar ta ya d’aure mata gashinta da tuni ribom din ya cire, shima ya daidaita kansa yayi gaba yana fad’in’ “minti biyu”.
Cikin sauri har tana tuntub’e tasha gaban sa, bakin da yaga ta cunno harda rik’e k’ugu yasa yasan akwai darun da zatai masa.
Cike da sha’awa yake dubanta, ganin bai ce komai yasa ta k’ara d’ane bakin cikin shagwab’a tace” ni gaskiya babu inda zakaje ba zaka kaita ba”, ta janyo shi ta zaunar kan sopa,
“Zauna nan ni zanje muyi sallama in dawo”.
Dariya sosai yayi harda mirginawa don jin dad’i wai yau shi Deeja ke Adanawa a d’aki don kishi……
#Team Deeja ko tabarshi ya sauke ta?😜
SAFHA……✍🏻
[4/6, 8:52 PM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
©*SAFHA*
27-Tsaye tayi rik’e da k’ugu a tsakiyar falon tana bin ko’ina da kallo cike da mamaki, don ganin falon a gyare tsaf kamar ba wanda ta tuttulawa kananzir d’azu ba,
“Kenan gyaran gurin nan Muneera tayi shiyasa naji ta shuru tun d’azu?” Ta fad’a a fili,
Nan ta sauke idon ta kan akwatunan dake jere a gefe an cire ledarsu data b’aci da kananzir an goge su sai zuba k’amshi suke kmr yanda falon ke k’amshi kamar kwayar kananzir bata zuba akai ba.
Cikin hanzari tanufi tsakar gidan waiko zata tadda Muneera acan, wayam taga filin tsakar gidan, tad’an kira sunanta taji shuru wannan ya nuna mata Alamun ta tafi kenan, don haka tai murmushi cike da nishad’i takoma ciki.
A tsaye jingine da jikin k’ofar d’akin baccin su ta taddashi don haka saitayi tsaye takasa k’arasawa inda yake ta kuma kasa komawa inda ta futo,
Wani mayen kallo yake binta dashi Wanda ya saukar mata da kunya ta sunkui dakai tana murmushi ta gefen ido take satar kallon sa,
Cikin muryar da yasan zata kwance notikan nutsuwar ta ya soma magana a yayin daya tunkaro ta,
“Ki bud’e idonki ki kalleni da kyau ni Kamal nakine ke d’aya kikau da kunyar ki ki bani abinda nake buk’ata” zuwa yanzu ya iso gabanta ganin yazo daf tai saurin juya baya don wata kunyar sace ta dirar mata,
Ganin hakan yasa ya rungumota ta bayan yana goga fuskar sa jikin wuyan tana murmushi,
” najima da sanin Deeja na tana da buri hakane?” Yaciga ba” ki bani had’in kai nacika mana burin mu nima yanzu *INA DA BURI*”
Cikin sassafar numfashi don wasan daya somai mata yafara sanyata jin sauyi, da kyar ta furzo kalmar,
” meye burin ka?”
A yanda tai maganar ne yak’ara kunno shi don haka ya canja salon wasan a yanai mata rad’a a kunne,
Cikin jin kunya ta tsille tana ‘yar dariya ya rik’ota, ” ki tunan naki burin”
“Aa nayafe” tafad’a tana son zame rik’on dayai mata,
Sosai ya kuma rungume ta, ” kinji nawa burin ina son jin naki”
,”Burina a yanzu ina son naga kana farin ciki, inason nai maka biyayya Donna fahimci hak’uri ladabi biyayya suke inganta soyayya, rashin su na gurb’atata kuma ba soyayya kad’ai ake buk’ata kad’ai cikin gidan aure ba kamar yanda nake d’auka ada ba”
Ya gyad’a kai” uhm ina jinki”
“Shikenan buri na nidai”
“Aa ban yarda ba akwai wani, buri na shine naki, bazan bari kunya ta danne muradin kiba kamar yanda take danne muradin wasu ma’auratan’
Zuwa yanzu batada damar magana sai” hmm” Kamal d’inta yawuce duk inda take zaton sa.
Yacigaba” kifad’amin me kika tanadarwa soyayyata?”
Runtse ido tayi ta had’iye yawu da kyar ta saita nutsuwar ta”
“Zanyi tattalin ta, zan raineta, zan ingantata,zan shimfid’a mana rayuwa mai dad’i wacce zakai alfahari da ita, zan so nafika son kanka domin kai nawane zanfi samun tagomashin soyayyar ka kasancewar ka mallaki na, zan baka duk soyayyar da kake buk’ata koma fiye da hakan nidai ka rik’eni amana na sadaukar da burina gareka, jin dad’ina Kaine, farin ciki na kaine, kai ni komai nawa nakane ina sonka Jamal!”
Tsam ya rungume kayan sa, yana share hawayen ta da harshen sa,
Murmushi tasaki donjin furucinsa,
” nasani Deeja na aminta dake zaki aikata abinda bakinki ya furta, ina sonka Deeja na,’yar soyayya mai son soyayya mai iya soyayya mai burin soyayya, ina Alfahari da wannan na kasance d’an gata inaiwa Allah godiya daya bani Deeja mai sona mai son abinda nakeso kuma nake buri, kisa mana ranar tariya wasu lamuran sai a sabon gidan ki ko?”
Cikin murna da farin ciki tareda nishad’i suke darawa junan su,
” kasa mana rana mai sona”
Kyautar sumba yabata don jin dad’in sunan data kirashi dashi.
“Kwana biyu yayi miki Amarya ta?”
Ta zaro ido,” saurin meye hakan?”
“Rayuwar soyayya” yabata amsa cikin kashe ido,
“Sati d’aya mai sona kafin sannan mungama shirinmu ko?”
“Hakan yayi muje ciki kiji wasu batutuwa”
Nan tasoma zamewa tana fad’in” ainaji komai anan ni a falo zan kwana ma”
Cak ya d’auke ta ganin jan zare zatai tareda fad’in,
“Darasin ciki yafina nan dad’i”
Ta sak’alo hannayen ta wuyan sa cikin salon so tace” katuna kai yaya ne fa”
“Bazan gane ba hakan ba yanzu muk’arasa ciki ki ganar dani”
Dariya sukai baki d’aya a daidai lokacin dayasa k’afa ya turo k’ofar,
Asuba tagari.
****
Cikin wannan satin suka tsara yanda tariyar zata kasance, suka tsara walimar taya murna shagalin da ba’ayi na auren suba shine zasuyi k’ara’i ranar don haka cikin satin basu samu zama ba, sunata zirga-zirgar k’ara gyare sabon gidan su tareda k’awata shi don Sufi jin dad’jn more lokacin su,
Kuyi hakuri da wannan, rashin caji yasa,
*SAFHA*✍🏼
[4/7, 8:41 PM] Sdy Jegal: *INA DA BURI*
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION
©SAFHA
28-Walimar tariyar tasu ta tsaru yanda suke buk’ata, anci ansha anchashe don har y’an kid’a suka dauko suka wak’esu, walimar ta k’ayatar anyita cikin nishad’i da kwanciyar hankali, kulawar da suke bawa junan su cike da mutuntawa da d’inbin k’auna tareda soyayya yasa ‘yan uwa da abokan arziki da sukasan badak’alar da akasha da Deeja akan auren da kuma wahalar da Kamal yasha gun Deeja duk adalilin Burin ta yasa su mamakin k’aunar da tashiga gwada masa a wannan lokaci,
Hakan yayi musu dad’i don Mmn Ihsan dasu Muneera kusan sunfi kowa murna, sai kuma su mamy da labarin yaje kunnan su tunkan atashi daga walimar,
Duk wani masoyin khadeja zai tayata murnar samun gwarzon Namiji kamar Kamal wanda ya nunawq duniya Deeja tasace mallakin sa mai sonsa kuma abin Alfaharin sa.
Sun tsinci kansu cikin rayuwa mai dad’i wacce ko a mafarki basu tab’a tsammanin zasu riski kansu a cikin taba, wacce ta shallake tunanin Deeja ta tsere rayuwar da burin ta ke gwada mata.
A nasa b’angarenma yana jinjinawa jarumtar ta don Deeja maca ce d’aya tamkar da dubu babu inda ta kuskuroshi Ashe da kallon kitse yakewa rogo?.
***
Suna tsaka dajin dadin rayuwar su ne tafara zazzafan laulayi wanda ko minti biyar kukai tare da ita saika san halin da take ciki,
Cikin wannan tsakanin aka fad’a hidimar bikin Yaya Salis da Munneera, taci burin bikin taso tayi yanda takeso ayi sha’anin biki da ita kasancewar tana tsaka da laulayi a kwance cikin k’uryar d’akin Mamy tayi bikin ko futowa batasan yi sabida tsiyar da abokan wasa ke mata,ga kamal dake manne da ita a waya shiga d”ari futa d’ari saiya lek’ota shiko kunyar tsiyar da jamaar gidan suke masa bayaji da anyi magana yace” nifa banason sa ido” da wannan yake kashe bakin tsanya.
*****
Bayan shekara biyu.
Zaune suke saman kafet sunsaka yaran su a tsakiya Wanda suke zagaye da kayan wasa duk Wanda ka kalla cikin su kasan basa tare da matsala sunyi wani irin kyau Alamun Hutu da kwanciyar hankali ya bayyana a jikin su,
Dukkan kulawarsu na kan yaransu wanda suke kira da Shuraim d’ayan kuma Aeman, kyawawan yara masu kama da Mahaifin su, babu inda suka barshi siffar shi ta dogon bafulatani mai d’an haske da kwantacciyar suma sun kwafeshi tas,
K’auna,Soyayya,Aminci, ladabi biyayya da kuma mutuntawa ita tajagoran ci dorewar farin ciki cikin rayuwar su mai inganci, suna Alfahari da junan su sun kuma tabbatarwa da juna ruhi d’ayane gangan jikince ba d’aya ba,
Deejan kamal, kamal na Deeja, kai Allah yakara dankon soyayya yabarmu da masoyan mu na gaskiya.
Tammat bihamdillah,
Anan muka kawo k’arshen wannan littafi INA DA BURI!” ku tareshi a gaba cikin labarin KE CE TAWA!.
ALHAMDILILLAH.
godiya ta tabbata ga ubangiji sammai da k’assai majib’icin lamuranmu da kabamu ikon kammala wannan littafiKuskuren dake cikin sa Allah ka yafemana, Allah kabamu ladan alkairan dake cikin sa.
SADAUKARWA,
Ga d’aukacin masoya wannan littafi da wanda muka sani dama wanda bamu saniba, Allah yasaka da Alkairi yabar kauna ya kara kusantamu da masoyan mu na gaskiya ya nesan tamu da mak’iyan mu.
JINJINA GAREKU.
Iyalan gidan nagarta,Allah yasaka muku da Alkairi yakara hade kawunanmu ya doramu akan makiyanmu.
GAISUWA TA MUSAMMAN.
SDY JEGAL FANS
MOMHANIF NOVELS
ZAUREN MOMHANIF
FEENAT JAFAR FANS
ZAUREN KARATU
MUSHA KARATU
MOM FARTY NOVELS
MUMBARIN JABO
Dama sauran grps din da ban samu damar sawa ba, godiya muke Mara adadi👍
Sai munhadu a littafi nagaba!!!
SAFHA✍🏼